Hukumar EFCC ta kwace fasfot din surukin Atiku
Hukumar yaki da cin hanci da hana yi wa tattalin arziki
zagon kasa (EFCC) ta kwace fasfot din surukin tsohon mataimakin Shugaban kasa
Atiku Abubakar, Abdullahi Babalele. Ana bincikensa ne akan zargin satar kudi da
yawansu ya kai kimanin Euro miliyan 150.
A jiya Talata, 5 ga watan Maris ne aka
bayar da belin Babalele bayan ya sha tambayoyi na kimanin sa’o’i 72. Ana
bincikarsa ne tare da Mista Uyi Giwa-Osagie wani hadimin Atiku wanda hukumar ta
fara kamawa.
Hukumar EFCC ta kwace fasfot din surukin Atiku Source: Facebook
Sai dai har yanzu hukumar yaki da rashawar na rike da Uyi a daidai lokacin kawo
wannan rahoton saboda “har yanzu ana kan bincike ne”.
Wata majiya na EFCC wanda ta nemi a boye
sunanta tace: “An bayar da belin surukin Atiku amma bias wasu shariuda da suka
hada da kwace fasfot dinsa. Binciken da muke yi kan zargin da ake masa ya
bukaci da mu hana duk wani zirga-zirgansa a kasar.
“Za a ci gaba akan haka har
sai an kammala binciken da ake kan yi.” Da yake amsa wata tambaya, majiyar ya
kara da cewa: “Ana ci gaba da tsare Mista Uyi Giwa-Osagie wanda yake hadimin
Atiku ne a Lagas.
Ba zan iya cewa ga lokacin da za a ssake shi ba. “Amma dai
mun bayar da belin tsohon ministan ayyuka na musamman, Alh Tanimu Turaki.”
0 Response to "Hukumar EFCC ta kwace fasfot din surukin Atiku "
Post a Comment