CANJIN YANAYI 1



DAGA Maryam Adam ©MARYAM ADAM
GODIYA
Godiya ga Allah mad’aukakin sarki mai kashewa mai rayawa, maji6incin bawanshi, mai juyarda al’amurra yanda yaso a kuma lokacinda yaso, daya bani ikon koma d’ora Alk’alamina domin sake kawo maku wannan gajeren littafin, kuskuren da ke ciki Allah ya yafe min, yasa kuma sak’on ya isar muku cikin fahimta da hange.
YABO
Gareku d’aukacin masoyana dake nunamin so a gabana ko a bayana, nagode sosai Allah yabar k’auna a tsakaninku, da fatar zaku fahimci cewa nima ina sonku.
JINJINA
Gareku
Abdul-Majid, Abakar, Hamza, Abdul-Karim
                &
Maryam Adam (Hajiya).
TUKUICI
Tukuici ne gare Ku Y’an uwana na jini, Allah yakara mana dank’on zumunci da taimakon junanmu har zuwa kan Y’ay’anmu.
KE TA DABAN CE
Zulaihat (Mmn Jafar) A duniya inason mutum mai karamci daya san karamci kuma yake bawa karamci muhimmanci, wanda baya raina kad’an yake godiya ga abu komai k’ank’antarshi, bakina bazai iya furta gurbinki a zuciyata ba, nagode nagode nagode, Allah ya d’orar da zumuncinmu ya sadamu da juna ra’ayul Ayn.
        “Abban Farha yau a ina za’ayi ma shimfid’a, bedroom ko filin gida?, saboda naga yau garin da d’an alamar sanyi ba kamar jiya ba”.
Ruwan da ke cikin cup ya d’an kur6a kad’an sannan ya kallota da gefen ido ya furta’ “kiyi shimfid’ar filin gida”. Har ta kai k’ofar fita waje d’in komai ya tuna ya bud’a baki yace’ “Zainab yi shimfid’ar a bedroom”.
Hakan ta koma bedroom d’inshi ta yi shimfid’ar ta fito gefenshi ta zauna, “ina fatar kin kunna A.c d’in?”.
“Aah”, ta bashi amsa a tak’aice.
Nan ya tashi ya shige bedroom d’in ya kunna A.c kana ya fito gurin suka cigaba da tad’i.
Hawaye take yi har ta kai ga shiga d’akinta, kwance ta yi rub da ciki tana kuka har da ajiyar zuciyarta, saboda tana jin zafin yanda Abban Farha ke nuna banbanci a tsakaninta da Zainab, ta rasa gano cewa me yasa duk ranar girkinta zai ce a fitar da shimfid’a daga waje, amma ranar girkin Zainab sai dai su shige bedroom d’inshi su kunna A.c suyi kwanciyarsu, bama wannan ba in ma ba Nepa koda yana cewa baida kud’i a hannunshi hakan bazai hanashi siyen mai da zai tada gen ba.
Sannan ga wani babban abinda ke ci mata tuwo a k’warya duk ranar girkinta ba zai ta6a lamunta cewa tayi wanka d’akinshi ba, sai dai yace taje nata d’akin tayi wanka sannan taje d’akinshi, amma tun ranar da ya auro Zainab sama da shekara biyu idonta basu ta6a hasko mata ita tayi wanka daga nata d’akin taje nashi ba. Dama a duniya yawanci ba kishiya suke gudu ba, bak’in halinta ko kuma sauyi daga Maigidan, ma’ana ya nuna banbancin a tsakaninku na zamantakewa, amma in ba wannan ba kishiya y’ar uwa ce.
(Anan zan so naja hankalin mata y’an uwana kan cewa Ku rage d’orawa kanku mugun zafin kishi akan kishiya, wallahi muddin Allah ya k’addarto ba zaki rayu da Mijinki ke kad’ai ba to duk dad’ewar da kika yi dashi wallahi sai ya yi auren, wani lokaci ma sai kin fara tsufa yara sun sakaki gaba sannan yaje yayi aure, kuma a lokacin ke yara zasu tauye a wasu abubuwan shi ba ruwanshi wallahi don jin kanshi yake tamkar wani sabon Ango, kinga ko hakan bai yi tasiri ba na hanashi auren da kika yi da wuri ba.
Magana ta gaba itace, cewa ni kishiya bata da rana gareni, ko hanyar da kishiya tabi bana so nabi wallahi lolx, masu irin way’annan maganganun na bani dariya sosai wallahi, shin kin manta cewa akwai ciwo akwai mutuwa ne Y’ar uwa?.
Ku k’iyasta da kanku kuga, lokuta da dama lalurar ciwo zata sakaki gaba wacce wallahi wani lokaci ko Maigidan bazai riga kishiya kawo agaji zuwa gareki ba, yau ko ciwo kike ta taimakeki da ak’alla ko ruwan sha ne to kinci cikin kishiya kuma ta yi maki rana, wani lokaci ciwo zai zo maki na ko wayar ba zaki iya d’agawa ki kira Maigida ko wani d’anuwanki ba, a wannan lokacin ke kanki ba zaki san yanda akayi kika k’walla mata kiran neman agaji ba, in kinyi tunani nan ma ta taimakeki.
Wasu suna amfani ne da cewa naga anyiwa wance kishiya ta wulakanta, ko Aah a gidanmu an yiwa Mamata kishiya ta wahala, ko K’awarki da sauransu wannan ba hujja bace kowa da yanda aka rubuto tashi k’addarar, abu d’aya nakeso kuyi amfani dashi addu’a da kuma tawakkali, addu’ar kuwa itace in har ina daga cikin mutanen da zasu zauna da kishiya Allah ka datarda ni data gari, kuma kar ka bani ikon zalunci akanta ko ka bata ikon ta zalunce ni, kuma ki zauna da ita da zuciya d’aya wallahi wallahi wallahi Allah bazai barta ta zalunceki ba, in ma tayi to kad’an ne kuma zai bi maki bashi, saboda haka don Allah mu rage zafin kishi da zai iya kaimu ga halaka.)
Tun tana tunani a ranta har bacci ya d’auketa wanda kiran Assalatu ne ya tada ita har tayi sallah ta koma bacci wanda ba ita ta tashi ba sai wuraren k’arfe goma inda taci karo da Zainab ta fito daga d’akin Abban Farha tana wani yatsina an shar6ar da gashi da ruwa ana gogewa da towel, saurin kautar da kanta tayi ta shige kitchen domin d’ora ko ruwan tea ne ta walwale hanjinta.


SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "CANJIN YANAYI 1"

Post a Comment