INA DA BURI kashina 14

*INA DA BURI*
MARYAM ADAM
FEENAT JA’AFAR
            &
HAFSAT ISMAIL (MMN HANEEF)
_Yan Uwa muna barar addu’arku zuwa ga yaronmu Muneeb, Allah ya bashi lafiya ya d’auke lalura, da sauran dukan musulmai baki d’aya_.
14_A tsaye yake hannu bisa ha6a yana dubenta fuska d’auke da murmushi lokacin da take kunjin kukan ruwan da tana ji tana gani ya matseta aka mamuka mata.
Kuka take harda shessheka,ta yarda Kamal ya wuce tunaninta,dan a fagen mugunta tasan in za ai competition toh ba abinda zai hana yazo 1st position.
Yau tun tana da karfi amma sai da ya nuna mata karfi gun amsar allurar karfi da yaji,Allah ya isa ta fad’eta tafi dubu acikin ranta,dan yanzu har tsoron fidda tsiwarta take a fili, dan tasan sai ya fanshe.
Tana nan har baccin dole ya sureta,in banda ‘yar harara ba abinda take aika mishi sai kuwa kuka,maganin karya kam,wai hallara.
Ido ta bud’e a hankali jin ‘yar hayaniya a kanta,Mamy ce da shi su na dubenta.
Baki ta fara ta6e wa halamun kuka ganin Mamyn.
Karaso wa yai hadda fad’in
“Sannu,kin tashi?
Kuka ta saka,dan haka sai Mamyn ta matso shi kuma ya hau k’ok’arin cire mata ruwan ya fuce.
Da dan tausayi Mamyn ta bita da kallo wanda ke nuna alamar duk ta fara zabgewa, nan kuwa Mamy bata san cewa zabgewar masifa bace da rashin kwanciyar hankali.
Sannu ta yi mata had’e da jefo mata tambayar lokacin Kamal ya dawo rike da kofin ruwa akan faranti 
“Koh dai laulayi ne ke damunki?…
Shiru tai,duk da Kamal din yaji zancen amma sai ya kalleta,da sauri ta girgiza wa Mamyn kai
“A’a ba shi bane..
Dariya Kamal din ya kunshe,a ranshi yana fad’in
”Wuya kenan..
Kai Mamyn ta jijjiga,
“Amma ance harda amai fa Deeja…
“Allah Mamy banda komai ciwo ne kawai, kuma ma naji sauk’i”. 
Kai Mamyn ta kad’a.
“Toh Allah ya kara afuwa.
Baki washe Kamal din ya ce 
“Amin Mamy, ga ruwa.
Ido Deejan ta kulle,koh kad’an bata son kallonshi tunda bazata iya gasa mishi magana ba.
Bayan Mamy ta d’an yi mata nasihar kula da kanta ta tashi Kamal ya rakata ta tafi, sannan ya dawo d’akin yana mai k’unshe dariyar mugunta.
Ido ta bud’e tare da kafeshi dasu.
“Wai mey ka ke nufi dani ne?
Zama ya yi tare da gyara mata filo.
“Abinda ki ke nufi dani My Deejalo.. 
Hannu ya kai gefen kumatunta zai ja tai saurin make hannun.
“Bazan ta6a yafe wa ba tunda ka zalunce ni, macuci kawai azzalumi mara tausayi, ai nasan fiye da hakan ma zaka aikata a kaina,mara tausayi, wallahi sai Allah ya saka min”..
Kuka ta saka,dan haka da sauri ya sha mur.
“Wato har yanzu kina da bakin tsiwa koh?
Banza tai mishi,cuta kam ya riga da ya cuceta,bakin cikinta d’aya kar wata cutar ta sameta tunda lafiyarta kalau.
Tun daga wannan ranar ta fara kama kanta,zai wuya ta tanka mishi sai dai harara daga nesa,dan ba karamin tsorata tai da sharrin Kamal ba da yafi na mata d’anuwa,ta nan kam ya samu sa’ida.
***
A gaban mirror take tana shafa mai had’i da dan harararshi,yayinda shi yake zaune kan gado sai murmushi yake yana shafa ha6a,yau kusan sati biyu tana mishi karyar period take,gashi yau ya kamata tana ruku’u.
“Wato baki daddara da karya ba koh?
Kalloshi tai tare da shan mur.
Shiru tai tare da cigaba da abinda take,dan ba karamin sanyi ake ba ga ta debo wankan da ya zame mata tamkar dole na dare.
Sakko wa yai,shi har ya yi missing tsiwar nan ta kwana biyu da ake mishi yanzu sai harara daga nesa.
Man ya dangwalo yana yana shima yana dan hararar tata.
“Ki sani lissafi za ai,dan wannan sati biyu sai kin ramata a yau…
Baki ta bud’e ganin wani karfin hali ganin ya riko hannunta yana shafa mata mai.
Zumbur ta mike tare da k’ank’ance ido zata fara bala’i ta tuno da karan baya dan haka sai ta matsa tare da fad’in
“Bana so,ka fita kuma harkata…
Tashi yai tare da janyota da d’an karfi ta taho gareshi.
“Karya ne wannan, dan haka kar ma ki wahalar da kanki.
Tureshi tai da sauri tare da matsawa ganin yana neman samo lagonta.
“Wai in ba kai mugunta ba baka jin dad’i ne?
Kai ya daga da sauri yana mai matso wa.
“Ai gunki na koya,koh kin manta?
Baya ta fara ja tana had’iyar yawu.
“Naji, duk da haka wallahi kar ka ta6ani..
Chafka ya kawo mata da sauri ta zille gefe.
Kai ta jijjiga,
“Wato so ki ke mu zama kullum Tom and Jerry koh? Wanda basa jituwa sai sunji jiki koh?
Kai ta kad’a da sauri
“Ai bazan ta6a jituwa da kai ba kasan wannan..
Tsalle ya doka tare da ritsata lungu.
“Nafi son haka,dan yana kara sa minke ladabin dole..
Magana zatai,sai dai kan ta kai ga furtawa ya chafkota,kamar kullum dai yau ma shi yaci nasarar sata lagwas,sanda komai ya lafa kamin ta hau kukan ya cuceta.
SAFHA…

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "INA DA BURI kashina 14"

Post a Comment