INA DA BURI Kashi na 2

*INA DA BURI 2 *

FEENAT JAFAR
SDY JEGAL
         &
HAFSAT (MMN HANEEP)
2_Idonta yayi jajir don tsabar kukan data sha, shikuwa Najib tsohon saurayin ta dake gefe yana faman aikin lalashin sahibar tasa, ya sauke gwauron numfashi kana ya ce
“Ni yakamata nayi kuka bake ba Deeja, ni banga ta inda Allah ya kuskuroni ba da kika kasa tsayar dani matsayin mijin aurenki.
Ido ta dago tana dubenshi galala,dan haka sai ya cigaba da fad’in
“Wai shin,ni soyayyar ce ban iya ba kome? 
Wani mugun kallo ta sauke masa cike yatsine fuska.
“Ka ga,nifa ban kiraka don ka zauna kanaimin shirme ba, kabani shawarar yanda zanyi donni gaskiya bazan yarda ayimin auren dole ba dan wannan baya cikin buri na”.
Tsayuwa ya gyara,
“To ni yanzu mezan ce miki khadeja? Kawai kije kicewa Abba ni ki ke so kinga kin huta da fargabar Wanda za a aura miki…
Shiru sukai ganin Abba zai shige kowa ya saukar da kai kasa.
“Abba ina yuni..
Dan rissina wa yai Abban yana binsu da ido.
“Lafiya Najib,ya mutan gidan?
Har su ka gama gaisawa Abba na hasaaso wani abu cikin ranshi.
Kai ta dafe tare da fad’in
“Ya ilahi..
Fatan ta Allah yasa kar Abba yai wa zancen su na yau fassara,dan haka da sauri ta ce
 “Kaga shikenan jeka inna nutsu zanneme ka,dan yau ba wani aikin da zaka min..
Kai ya kad’a yana mata wani kallo na Allah kai damo ga harawa ta shige ciki.
Kicibis su ka ci da Kamal a bakin kofar parlour duk su ka kallo juna rai a had’e.
Kauce wa ya yi da niyar ya bata guri itama ta koma inda ya koma,harara ta maka mishi da zummar sauya gu ya sake yin wajen dan haka a masife ta ce
“Malam ka ban waje na wuce..
Rai ya had’e ganin zata raina mishi hankali ya ra6a ta gefe ya wuce tana mishi harara.
****
“Ni fa ina ga yaran nan son juna suke Mamyn su..
Da mamaki Mamyn ta kallo Abba.
“Su wa fa?
Murmushi ya yi tare da gyara zama.
“Najib da Deeja nah..
Ido ta sa mishi,jin ba wanda ta hasaso ya hasaso ba.
“Najib kuma?
Kai ya jijjiga mata.
“Ina ga na samo mafita, abu d’aya nake tunani bai da aikin yi ban san da mey zai riken Deeja ba..
“Ni fa Alhaji ba Najib ya dace da Deeja ba,kamata ya yi ka had’a Deeja da wanda zai iya seta tunaninta ya juyata ba wai ita ta juya shi ba.
Ido ya sa mata yadda take bayanin,yasan inda ta dosa tunda an ta6o kishiyarta Deeja.
Dan haka da sauri ya katseta.
“Ban san mey Deeja ta tsare miki ba,kullum burinki ki ga yarinyar nan na kuka tamkar ba ke ki ka haifeta ba.
Baki ta saka tana kallonshi,daga fad’in gaskiyar?
Kai ta kad’a tare da jan bak’inta ta rufe,tasan yanzun tata zatai zafi.
****
Aure kam Abba bai fasa ba,duk wata dabararta ta kare daga Najib har Mariya kawarta ba mai wata shawarar da zata bulla mata.
Yau tafi kullum kuka ganin gobe iyanzu ta zama matar Najib.
Zumbur ta mike tare da fita a d’akinta ta nufi d’akin Abba,tabbas wannan ce damarta ta karshe,in ta bari aka aura mata Najib tasan tai babbar wauta a rayuwa.
Kuka reras ta tasa shi gaba tana yi,dan haka tuni ya rikice ya hau tambayar mey ne ne?
“Abba ni fa ka had’ani da kowa amma banda Najib…
Harshe ta datse jin ta kwafsa.
Murmushi Umman tai tana cigaba da dama furarta.
Kai Abban ya girgiza, 
“Matuka zan sa6a miki wannan karan Deeja,dan babu abinda zai sa na warware auren nan tunda har gobe ne za’a d’aura..
Bori ta hau mishi harda su shusshura k’afa.
Ya sani da matuka yana ji da ‘yarshi tilo d’aya mace tamkar tsoka daya cikin miya.
In har ba so yake zancen Baba Zubairu ya tabbata ba na tsoron Deeja yake toh kwa dole ya nuna mata aure ba fashi,dan haka kawai sai ya tashi tare da shige wa band’aki ran shi na kunar jin kukan nata.
Rarrafo wa tai gaban Mamyn.
“Dan Allah Mamy ki taimake ni kar a ban Najib,ni wallahi nafi karfin Najib,na yarda ni nake korar samarina amma dan Allah kar a ban Najib..
Baki Mamy ta saka,fatan ta Allah yasa Alhaji yaji wannan batu na Deeja.
“Na sani ai,ki d’auka wannan ne sakayyar su gare ki da Allah zai musu,baki fara kuka bama sai in kin ganki a gidan Najib din.
Kuka kam Deeja tasha shi,hannu bisa kai ta fio a dakin Abban.
Duk da kallo su ka bita duk su na sauraron ihun nata daga saman Abban.
Murmushi Kamal ya yi tare da girgiza kai.
A gaban yayun nata ta zube.
“Ya Salis dan son ku da Allah kar ku bari a min auren nan da Najib,wai ni yau Abba ya fatattaka…
Kuka ta sa musu,dan haka masu harararta nayi,masu kunshe dariya nayi.
A kaf gidan da wanda bai san halin Deeja bane,ai a ganin su wannan ne dai-dai tunda dama bata da abokin shawara sai Najib,dan haka a hankali kowa ya fara zame wa tana binsu da ido.
Kamal ne kad’ai ya rage wanda yasha mur yana kallonta.
Harara ta sau mishi duk da kuka take kamin ta mike tana goge hawaye zata wuce
“Ni kad’ai zan iya taimakon ki Abba ya janye auren Najib kin san wannan..
Chak! Taja ta tsaya ba tare da ta juyo ba,ta sani da tabbas matuka Abba yana jin shawarar Kamal.
“Ki sauke komai ki bishi ya taimake ki..
Kai ta kad’a jin shawarar zuciyarta.
A hankali ta juyo tana mai goge hawaye.
Ya hakimce a kujerar tamkar wani sarki yana dubenta,wannan ce yasan damarshi ta karshe da lalle Deeja zata shigo hannunshi.
Kasa ta zauna tare da kura mishi ido.
“Toh ka taimake ni..
Kallon tara saura kwata yai mata.
“Wannan ba ladabin roko bane..
Harara ta sau mishi tana had’e rai,sai dai tuno da shine damarta ta karshe yasa ta mike bisa gwiwarta tare da yin kalar tausayi da yanayin roko
“Dan Allah ka taimake ni yaya Kamal..
Murmushin mugunta ya saki tare da jijjiga kai ya mike
“Ashe kin iya ladabi yarinya..
Wuce wa yai ba tare da ya sake kallonta ba saman Abba,cike da takaici ta mike ji take tamkar ta shako shi ta huta,sai dai dole tai ladabi dan ita zai taimaka.


SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "INA DA BURI Kashi na 2"

Post a Comment