INA DA BURI kashi na 1

INA DA BURI* 
1   
®NAGARTA WRITER’S ASSOCIATION.
©{SAFHA}
MARYAM ADAM
FEENAT JAFAR
            &
 HAFSAT ISMA’IL (MMN HANEEP).
 Bismillahirrahmanirrahim
Godiya ta tabbata ga Allah subhanahu wata Ala daya bamu ikon fara rubutu lafiya ina rok’on Allah yasa mu gama lafiya, Ameen.
1_Babbar rigar sa ya sab’e tare da sa hannu ya bankad’e labule idonshi akan uwargidansa wacce suke kira da Mamy. Da d’an jimami ya soma magana 
“Kinga mutanen nan ko? har yanzu shuru ba busu babu dalilin su. 
Baki Mamy ta d’an ta6e
“Uhm to ni meye nawa a ciki Alhaji? In dai Khadija ce toh idone nawa in an maimaita irin ta wancan karan.. 
Da sauri ya daga mata hannu tare da fad’in
“Kar ki mana mugun fata,tuntuni nake fad’a miki wannan zantutukan naki su suke tasiri akan Deeja”..
Baki taja ta rufe fuskantar bazai gane inda ta dosa ba.
“Ka d’ai kirata ka ji ta bak’inta, dan na tabbatar tasan abinda ta kulla..
Jim yai tare da sawa Mamyn ido,zancenta da kamshin gaskiya,dan haka wannan karan sai ya kwala kiran Deejan.
Da nutsuwa ta fito fuskarta babu yabo babu fallasa ta zauna gaban iyayen nata.
Abba ne ya gyara zama tare da fad’in
“Nace ya kukai da shi Aminun kinji da kyau kuwa yau din za suzo akan maganar auren naku?”.
Kai ta dago tare da d’an sato kallon Mamy dake kallonta sai tai da kai kasa.
“Abba ni banyi waya dashi ba tun shekaranjiya, jiya ma naita kiransa kuma bai d’aga ba… 
“Hmmm,kuma dai..
Mamyn Abba ya kallo
“Meye na wani hmm? Kinga indai bazaki fadi Alkairi ba to kiyi mana shiru”.
Hannu ta aza bisa bak’inta halamun tai shiru.
Shi kanshi Abban al’amarin Deeja na bashi ciwan kai,sai dai so ya hana ganin laifinta.
“Ni fa bansan me naiwa Aminu ba shekaranjiya k’alau muka rabu dashi da yamma wallahi Mamy”..
Baki Mamyn ta ta6e halamun meye nata aciki duk Abban na kallon su.
Chan dai ya ce
“Kinga bani lambarsa nakirashi da kaina, in aka bibiya ma suna hanya gosulo ya tare su”…
Baki Mamyn ta saka tana duben Abban lokacin da Deejan ke miko mishi waya d’auke da numbern Aminu bisa screen.
Aminun ya kira,sai dai har ta gama ringin ta katse Aminu bai dauka ba har karo na uku.
Cike da mamaki ya sauke wayar tare da ciro tashi ya hau diban numbern zuwa tashi.
Deejan ya mika wa tata tare da sanya tashi bisa kunne halamun calling.
Bugu d’aya biyu Aminu ya d’aga wayar wanda ke kwance saman gado ya tasa hotunan Deeja a gaba yana jero mata Allah ya isa tun a daren jiya.
Sallama yai yi cikin sassanyar murya,take Abban ya shanye mamakinshi ya amsa sallamar.
Daga can b’angaren Aminu ya gyara zaman wayar a kunnan sa
“Wa ke magana?”.
Cike da kunar rai Abba ya ce
“Isma’il ne Mahaifin Khadeeja…
Mike wa Aminu ya yi cike da girmama wa yana gaida shi.
Sassauto wa Abban yai tare da amsawa,
“Dama munji shiru ne ga jama’a na jira daga chan gurin naku..
Jim Aminun ya yi,bai isa ya cewa Abba kanshi tsaye ya fasa auren Deeja ba,dan haka sai ya hau kame-kame
“Um dama Abba cewa nai a bari na kuma shisshiryawa a tsanake in yaso in Allah ya kaimu wani watan sai naturo ayi maganar auren ina neman wannan alfarmar Alhaji”.
Jim Abban yai,tuni ranshi har ya fara kuna jin zancen Aminun naso ya mayarshi karamin yaro,dan haka ya ce
“Shekara biyar tayi maka?
Kai Aminu ya girgiza da sauri kamar Abban na kallonshi
“A’a Abba,hak’uri za ayi akwai shirin da nake yi insha Allahu…
Kit ya kashe wayar ba tare da ya jira zancen Aminun ba rai na tafasa,tabbas yasan karan nan ba laifin Deeja ba ne.
Kallota yai yadda ta fara waro ido tana kallonshi.
“Ke dama wannan yaron d’an k’ananun mutane ne masu baki biyu baki sanar da niba tun wuri sai da na tara jama’a yanzu?
Kasa tai da kai, sai ya kallo Mamy wacce nata ido da kunnuwa.
“Mey zanje na cewa mutanen nan?
“Tabbas wannan abu akwai rashin kyauta wa aciki.
“Alhaji.
Ido ya sa mata
“Ya fa kamata ka tuhumi Khadija ko akwai tsiyar da ta shukawa yaron nan,ni nasan Aminu yaron kirki ne kasan babu yanda za ayi haka kurum yace ya fasa auren nan..
Ido Deeja ta zaro tare da kallo Abban,haka yasa a hassala ya ce 
“Mey ki ke nufi kenan? Kina nufin laifin Khadija ne duk da kinji abinda ya ce?
Kai Mamyn ta girgiza tare da fad’in
“A’a, ni bance ba,dan haka Allah ya baku hak’uri..
Fuska Deeja ta marairaice tare da yin narai-narai ido kamar za tayi kuka 
“Abba,wallahi ka yarda bansan me naiwa Aminu ba shekaran jiya k’alau muka rabu fa…
Harara Mamy ta doka mata cike da takaici,kan ta kai ga magana Salis ya shigo.
“Abba su Baba Zubairu fa sun k’osa da jira. 
Ajiyar zuciya Abban ya sau,nan ya sanarshi abinda ya faru.
“Abba to ajira shin kamar yanda ya ce d’in ko akwai matsalar data tsai dasu”.
Kai ya hau girgiza wa,
“A watan nan da nai alkawari a shi zan  aurar da Khadeeja bazama takai watannin daya d’iba ba balle yayi tunanin jiransa ta zauna yi, in alfarmar yake nema meya hanashi ya nema tun kwanaki sai yau da muka zau…
Hannu Deeja ta aza bisa kai tana kallon Abba ido a ware wanda ke sababin zai bawa Aminu mamaki.
Tuni taji gabanta na fad’uwa ganin a yau tai gudin gara gashi zata tadda zago.
Mamy ta kallo wacce ke murmushi tana kad’a kai tare da bin su Abban da ido.
Tabbas yau karya ta k’are.
Sumumu ta mike tana tafe tana had’a hanya,
“Yaushe za a gane wai ni Deeja *INA DA BURI* ne?
Da6ar ta zauna bakin katifar d’akinta hawaye na zuba.
 Hannu ta aza bisa kai tare da sakar ihun kuka na tuno da shin wa Abba zai bata?
Tasan ta kad’e har ganyenta in har aka bata wanda bashi take da buri ba.
****
Hak’uri Abba ya bawa yayun nashi da sauran y’an uwa had’i da sanar su abinda ya yanke,a take su ka goyi bayan shawarar kan a aurar da Khadija dan huce takaicin Aminu da ‘yan baya.
***
Futowar shi kenan daga d’aki kasancewar asabar ce ba zuwa aiki ya jiyo fad’an Mamyn, ko ba’a fad’a ba yasan itada Khadeeja ne don haka kai tsaye ya nufi cikin parlourn.
Kuka wiwi ya samu tanai a gaban Mamy,da ido ya bita yana mai kallon Mamy da halamun tambaya.
“Ai dama nasan bani da kaffara Kamal,tabbas Khadija na da hannu gurin rushe duk wani shiri na aurenta in har ya taso.
“Dan bani da abinda zan iya miki,dan fa duk tsuntsun da yaja ruwa shi ruwan kan doka..
Kai Deejan ta dago ido jajir tare da maka mishi harara,in har taki jinin wani a gidan,toh Kamal ne,dan haka cike da kara tusa haushi ya sau mata murmushin mugunta Mamy na kallonsu.
Tashi Mamyn tayi tare da yin hanyar kitchen, cike da keta ya kallota wacce har yanzu hawaye take goge wa kanta kasa.
“Irin ku ai dama a auren sadaqa ku ke karewa garin ruwan idon *INA DA BURI*..
Chak kukanta ya tsaya tare da kalloshi ba koh kiftawa.
Kai ya d’auke daga kallonta, dan haka sai tai murmushi irin wanda yau tare da fad’in
“Ban yi kama da matan da za ai sadaqa dasu ba kasan wannan.
“Sannan duk halina bai kai na mai auren auri saki ba dan haka bazai zama laifi ba in har na ce nima *INA DA BURI*…
Da sauri ya kallota,tabbas yasan magana ta ya6a mishi had’i da gori kamar yadda ta saba in taso sa shi a bakin ciki.
Yau ma kamar kullum yai tsam tare da kallonta,bai san meye laifin Babanshi zai rika zama makamin da za’a rika dukanshi dashi a kullum ba yana jin haushi..
Duk tsiya yasan iyaye-iyaye ne,ba kuma a sauya musu suna,dan haka yana jin ciwo in har Deeja ta ci mishi fuska akansu..
Murmushi ya yi tare da gyad’a mata kai.
“Hakane,zan so ya kasance a ni za a bawa sadakar aurenki Deeja.
Rai ta had’e kamar yadda yai tsammani da sauri,dan haka sai ya girgiza kai tare da fad’in
“Mai da wukar,dan koh a k’afa aka d’aura min ke bazan iya ja ba,sannan nima *INA DA BURI* bana jin kina daga cikin shi..
Tashi yai ya batta baki sake dan tsabar takaici, da kallo Mamy ta bishi wacce ta fito a kitchen sarai ta ji su har ya fuce.
 Deeja ta kallo wacce ke kumfar bak’in
“Ubangiji ya tsareni ni Deeja,koh a mafarki ba za kaga wannan ranar ba wallahi, mugu kawai mai mugun fata..
Tashi tai tare da shiga d’akinta cike da kukan takaici.
Tsam Mamy tai tana tunanin wani abu cike da sarkakiya,kai ta jijjiga tana murmushi dan jin shawarar zuciyarta.
Ku jira mu.


SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "INA DA BURI kashi na 1"

Post a Comment