INA DA BURI kashi na 15
*INA DA BURI*
MARYAM ADAM.
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSA(MAMAN HANIF).
15_Harara ya sau mata tare da fad’in
15_Harara ya sau mata tare da fad’in
“Saura carry over..
Baki ta saka,kan tai
magana ya chafki bakin dan sa mishi sakata,wuya kam tasha ta yau,sanda ta rika
rokon ta daina karya dan Allah yai hak’uri tukunna ya kyaleta yana gyad’a kai
na mugunta.
Gaskiya ta fara tsoron Kamal,ketakar shi mugun yawa gareta in har ya furta,dan haka tuni ta ajiye makamenta tai surrender, dan komai zata mishi,toh Insha-Allah kanta abin zai kare,dan ita ke jigata.
Gaskiya ta fara tsoron Kamal,ketakar shi mugun yawa gareta in har ya furta,dan haka tuni ta ajiye makamenta tai surrender, dan komai zata mishi,toh Insha-Allah kanta abin zai kare,dan ita ke jigata.
****
Zaune take bisa gado ta tankwashe kafarta tana dubenshi,da ya kallota sai ta dauke kai tare da ta6e baki.
Zaune take bisa gado ta tankwashe kafarta tana dubenshi,da ya kallota sai ta dauke kai tare da ta6e baki.
Link yake sawa na
riganshi gaban mirror yana dan mata murmushi, sosai yai kyau cikin fararen kayan
halamun zashi sallar juma’a ne.
“Ki fito ki ce ‘Habeebi kai kyau’ kawai ba ki tsaya satar kallona ba..
“Ki fito ki ce ‘Habeebi kai kyau’ kawai ba ki tsaya satar kallona ba..
Sama da kasa ta
kalleshi kamar taga kashi tare da ta6e baki.
“Allah sauka min,dan
ni dai banga kyau anan ba sam..
Murmushi yai tare da gyad’a kai tare da sanya hula ya tako gaban gadon tare da d’aukan sallaya.
Murmushi yai tare da gyad’a kai tare da sanya hula ya tako gaban gadon tare da d’aukan sallaya.
“Kyaji da shi dai,wai
gad’a a makabarta,ni na wuce,zamu dawo tare da su Salis.
Baki ta ta6e tare da
shirin magana ya dan mako bakin yana harararta.
Da hararar ta bishi har ya fuce hannu bisa baki,a hankali ta ce
Da hararar ta bishi har ya fuce hannu bisa baki,a hankali ta ce
“Mugu kawai…
Kai ya leko dashi tare
da fad’in
“Mey ki ka ce?
Ido ta waro, ba dai
wai yaji ba?
Da sauri ta girgiza kai tare da fad’in
Da sauri ta girgiza kai tare da fad’in
“A dawo lafiya na ce..
Murmushi ya yi tare da
kanne mata ido d’aya
“Sai na dawo.
Yake tai mishi, dan
haka sai ya tafi yana jijjiga kai,tabbas Deeja tai laushi wajen tsiwa,abu d’aya
ne taki ta sauke,ta kuma ki ta kalleshi a matsayin masoyi sai babban makiyinta.
*****
“Ni dai ina rabaki da wannan dabi’ar ta kafiya wallahi, ace ni na samu kamar mijinki k’awata wallahi babu mai jin kanmu..
“Ni dai ina rabaki da wannan dabi’ar ta kafiya wallahi, ace ni na samu kamar mijinki k’awata wallahi babu mai jin kanmu..
Baki ta ta6e tare da
gyara zama.
“Kin san Allah Kamal
bai d’ad’ani da kasa ba,cuta ce an riga da an cuce ni,duk wata dabara da zai
sauwake min nayi amma ban samu mafita ba..
Shiru sukai ganin Kamal din ya shigo koh bud’e kofa basu ji ba.
Shiru sukai ganin Kamal din ya shigo koh bud’e kofa basu ji ba.
Da kallo ya bisu
halamun kamar yaji zancen su.
Kai ta d’auke tana
turo baki,yayin da Muneera ta duk’ar da kai tare da fad’in
“Ina wuni ya Kamal..
Fuska ya sake tare da
amsawa yana fad’in ya gida?
D’aki ya shige ya bar Deeja da harara cikin duhu.
D’aki ya shige ya bar Deeja da harara cikin duhu.
Kai Muneeran ta
girgiza,
“Ba koh sannu da
zuwa,wallahi ki sauya halin ki,ki guji ranar da zai gaji ya auro miki
wata,gashi ni neman tsayayye nake na rasa ki fa gode Allah..
Banza tai mata kawai
tana tunanin wani abu.
Kira ya mata,dan haka tana chunno baki ta tashi ta nufi d’akin.
Kira ya mata,dan haka tana chunno baki ta tashi ta nufi d’akin.
Ido ya sa mata,tamkar
dabi’a haka wannan shegen chunno bakin ya zame mata wanda yafi tsana shi
kam,dan haka cike da shan mur ya harareta.
“Ina abinci na?
Rai ta had’e tare da
rike k’ugu tana gunguni.
A ganinta wannan ai gadara ce,a zuciyarta ta ce wai ‘ina abinci na? Toh ban dafa ba..
A ganinta wannan ai gadara ce,a zuciyarta ta ce wai ‘ina abinci na? Toh ban dafa ba..
“Da ke nake.
Juya wa tai tana
bubbuga k’afa da kunkuni tai waje,dan haka da kallo kawai ya bita had’i da
furzar da iska.
Deeja kam halinta sai ita,da ya toshe nan zata 6ullo ta chan,gaba d’aya ta dagula mishi lissafi da duk wani tanadinshi a gidan aurenshi.
Deeja kam halinta sai ita,da ya toshe nan zata 6ullo ta chan,gaba d’aya ta dagula mishi lissafi da duk wani tanadinshi a gidan aurenshi.
Kai kad’a, gab yake da
ya d’au matakin farko dan saita tunaninta..
Da ido ya bita ganin ta shigo rike da faranti a hannu da abinci bisa kanshi har lokacin bakin nan a d’ane.
Da ido ya bita ganin ta shigo rike da faranti a hannu da abinci bisa kanshi har lokacin bakin nan a d’ane.
Sakkowa yai tare da zama,dan
haka sai ta kawo da zummar ajiye wa ya damko hannunta.
Kokawar kwacewa ta hau
yi tana nishi jin kam ya riketa kawai sai ta sau mishi kuka.
Baki ya saka, tun ma kamin ya kwad’e bakin shine zata mishi 6aci?
Baki ya saka, tun ma kamin ya kwad’e bakin shine zata mishi 6aci?
“Mey yasa a gaban kowa
sai ki nemi nunan ban isa bane Deeja?
Kukan gaske ta
fara,tare da fad’in
“Saboda bana sonka
ni,sannan ka sani *INA DA BURI* wanda kai ba zaka ta6a iya cika min shi ba,dan
haka ka sallameni na samo mai sona..
Ido ya zuba mata rai 6ace,kan daga bisani ya sau mata hannun tare da tashi.
Ido ya zuba mata rai 6ace,kan daga bisani ya sau mata hannun tare da tashi.
Da sauri ta cigaba da
binshi da fad’in
“Koh kashe ni za kayi
wallahi sai na fad’i dan dole nake zaune da kai,amma ka ki ka gane..
Waje yai ya batta nan
tana kunjin kuka,tabbas Deeja bata sonshi, hasashen zuciyarshi kam yau ya
karyata shi.
Da kallo Muneera ta bishi cike da bakin cikin halin kawarta.
Da kallo Muneera ta bishi cike da bakin cikin halin kawarta.
Tsaki tai mata tare da
zarar jakarta ta fuce itama a gidan,dan haka tuni ta kara jiniyar kukan nata a
ganinta ba wanda zai gane inda ta dosa,kowa bai kaunarta.
SAFHA…
0 Response to "INA DA BURI kashi na 15"
Post a Comment