INA DA BURI kashi na 6

*INA DA BURI6*
FEENAT JAFAR
          &
HAFSA ISMA’IL(MMN HANEEP).
6_Da asuba ta farka,duk da dama baccin rabi da rabi tayi tana tashi yin dube-dube na dangin kunama,ga duk ya cinye wajen kad’an ta samu ya bar mata ta ra6a.
Juyi yake shirin yi duk wuyanshi ya k’age da kwanciya gu d’aya.
Ido ya sa mata ganin yadda zauna tare da sanya kanta bisa kafafunta a haka take bacci.
Tausayi ta bashi ba kad’an ba,dan yasan tabbas ba tai wani baccin arziki ba yau.
Dan haka hannu ya kai da niyar kwantar ta kwala ihu tana raba ido.
Harara ya sau mata tare da fad’in
“Wai ke abin ihu bai miki kad’an ne?..
Da sauri ta ce
“Eh d’in..
Kai ya jijjiga tare da tashi tai zirif ta mike.
“Ina zaka?
Banza yai mata tare da d’aukan buta sai ta bishi tana wai waye.
“Mey ki ke nufi ne wai?
Rai ta had’e tare da fad’in
“Abinda ka ke nufi,kana nufin ni kad’ai zaka bari a kurumin dajin nan?
Ido ya sa mata,karshe sai koma wa yai sai da gari yai sha ta barshi yai alwala.
A kan su ta tsaya ana tatsar nono ‘yan mata sai kwankwad’a suke,fuska ta hau yatsine wa tamkar tai amai yana kallonta yana jijjiga kai.
Karshe itama sai wannan d’in tasha,dan fa biskin jiya aka sake kawo wa wai dashi za ai break.
Deeja kam taga rayuwa,wacce take ga in ta kara kwana uku tabbas sai dai a d’au gawarta.
Rafi ta raka ‘yan matan rike da abin diban ruwa.
Ido tai saurin zaro wa ganin ruwan da zasu dina ga nan shanu sunyi layi su na sha,su na k’auce wa karnuka su ka hau layi.
K’ak’arin amai ta fara tuno da jiya tasha ya kai rabi,dan takaici har da kukanta ‘yan matan na mata dariya.
Su na dawo wa ta tubure mishi ita fa sai an tafi sam shi kam yaki kula ta.
‘Yan matan ya tambaya sai su ka mayar mishi abinda ya sata kukan,wai akwai rijiyar dad’i tai hak’uri an jima za su je su debo mata sai dai da nisa ne.
Rayuwa kam Deeja ta ganta a rigar Mangwano,shi da kanshi daurewa kawai yake,kwanan su hud’u sukai haramar tafiya.
Daga wannan lokaci bata sake tanka mazauninshi ba koh kiran shi da d’an kauye,dan ya sanarta akwai rigar da tafi wannan, chan zasu.
Da harara kawai ta bishi,dan tasan tsaf zai aikata,mugu kawai.
Koh sati basu fi ba su ka tare a gidan hayar da ya kama kamin ya idda gininshi.
Ranar ansha kuka,sai dai fur iyayen su ka ce zamansu kam a nan ya k’are,haka tana ji tana gani aka tasa keyarta gidan Kamal.
****
“Bana jin zan ta6a yafe maka dan kai sanadin da duk wani hangena ya rushe.
“Ka sani *INA DA BURI*, amma ba irin wannan ba..
Baki ya ta6e yana gyara kwalar rigarshi.
“Chan ta matse miki kuma wannan, dan yanzu babban burinki ki san hanyar faranta min in har kina so na daga k’afa..
Harara ta sau mishi tare da fad’in
“Allah sauka min ni Deeja,ai yadda kai sanadin komai,dole komai ya shafe ka..
Murmushi ya yi tare da jijjiga kai tare da daga kafad’a ya fuce.
Da yamma Muneera tazo kawarta,
“Iyanzu kam ya kamata ki ajiye makaman yakin ki Deeja,ina gudan miki ranar da zaki kasance baki a tsuntsu baki a tarko,ki yarda ke ce ke da mukulin saita duk wani Burinki ya koma yadda ki ke so,dan za ki iya saita tunanin namiji ta yadda ba kya tsammani..
Baki ta ta6e halamun abin bai ahigeta ba.
“Muna nan da ke da sannu cikin ruwan sanyi sai Kamal ya gane bai da wayo..
Hannunta ta riko.
“Yanzu yana a matsayin mijinki ne,dole ki bishi in dai kina son ki tsira gurin Allah..
Hannun ta zame tare da fad’in
“Toh uztaza,mu bar wannan layin kawai..
Kai Muneeran ta jijjiga, tasan kawarta kam tai nisa, zai wuya taji kira cikin sauki.
Har ya dawo su na nan tare kamin tai musu sallama ta tafi.
Da harara ta bishi bayan ta dawo a rakiya ya bita da kallo,kai ya jijjiga,ya kusa saita tunaninta lalle.
Kimanin sati biyu kenan da tarewar su amma kullum sake 6otsare mishi take da wani salon.
Da dare ya yi zata sakace d’akinta sai dai yai kwanan parlour.
Abinci sai dai ya dafawa kanshi,yau dai ya kudiri aniyar saita wasu abubuwan,dan haka ya ce
“Ina abinci na?
Sama da kasa ta kalleshi a wulakance tana shafa mai
“Kai da wa?
Ido ya sa mata sam bai da walwala yau,dan haka a tunzure ya shige ciki tuni ta mike tsaye.
“Nai miki hak’urin sati biyu da kawaici ba kya gani koh?
Rai ta had’e da sauri ganin ya karaso tai band’aki da sauri ta datse tare da fad’in
“An fad’a baza’a dafa ba d’in.
Yin duniya taki ta bud’e, karshe 
 kamar kullum yau ma shi ya dafa.
Da daddare ta gama shirin kwanciya kamar kullum ta tashi zata rufe kofa ya danno kai.
Rai ta had’e da sauri had’i da rike k’ugu.
“Lafiya?
Juya wa yai tare da maida kofa ya rufe had’i da cire mukulli ya juyo yana kallonta.
Cike da in ina ta fara fad’in
“Na..na..ce lafiya?
Hannun riga ya fara tattare wa yana murmushin mugunta.
“Ki bari ai zan nuna miki koma meye..
Baya ta fara ja tana had’iye yawu kwat tana raba ido.
Kanta ya yi dan haka da sauri su ka fara ‘yar tsere cikin d’akin, fad’i yake
“Yau zan maganin ki,dan ni kad’ai zan iya miki kin sani,wannan fitsarar yau zata tafi garin su..
“Ba haka mukai da kai ba,bana ciki da mugunta…
Shiru tai ganin ya damko ta da duk karfinshi,tuni ta fara kukuwar kwace wa tana masifa.
“Wannan ai iskanci ne..
“A gunki na gani ai na koya..
Magana zatai yai saurin toshe mata bakin ta hau mutsu-mutsu, tun tanai har tai lakwas,dan haka da sauri ya janye kanshi su na maida numfashi.
Yawun bakin ta tattaro tare da tofarwa tana goge bak’in.
“Mugu kawai…
Murmushin mugunta yai tare da jijjiga kai
“Ke kuma munafuka ba,ai gwara ma ki shanye,tun dama abin neman ki ne ya samu,a kuma yau mai gaba d’ayan zai zo..
Matsa wa tai tare da nuno mishi kofa.
“Ka fitar min a d’aki malam..
“Kin biya kud’i ne da ya zama na naki?
Matso wa ya fara tana ja da baya,sosai yau kam ta gano ketar ce ta motsa,in kuma batai da gaske ba haka zai shata a banza, dan haka da sauri ta dawo sabuwar masifa.
Muje zuwa
SAFHA…..

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "INA DA BURI kashi na 6"

Post a Comment