INA DA BURI kashi na 8

*INA DA BURI8*

FEENAT JAFAR
          &
HAFSA ISMA’IL(MMN HANEEP).

*_Naki ne wannan, our dorling Dota Feedoh,(‘Yar Fichika)..saura 4*_
8_”A’a, Aunty amarya ce a gidan namu?
Murmushi tai tana d’aukan Ihsan.
Bayan sun gaisa ta d’au littafin da ta gani bisa kujerar Maman Ihsan na hausa tana duba wa,sosai ta nutsu cikin shi sai murmushi take ita kad’ai.
Kai Maman Ihsan din ta girgiza mata tana murmushi tare da ajiye mata plate din hannunta mai d’auke da ruwa.
“Haba,haba Malam,ki duba irin wannan soyayya da ake shinfid’awa a littafin nan exactly irin wacce nake da *Buri*.
Littafin ta ajiye tare da ta6e baki da marairaice fuska,
“Bana tunanin mugun nan zai iya rabinta,dan har gwara ma gidahuman chan su Aminu dashi…
Shiru tai ganin yadda Maman Ihsan din ta sau baki tana kallonta.
“Na tambaye ki man Deeja?
Kai ta jijjiga halamun tana ji.
“A yadda na fuskanta ke burinki a soyayya ya k’are,ba ruwan ki da sauran burin gidan aure sai wannan koh?
Kai ta daga mata da sauri.
“Sosai kuwa,dan ni fa akan wannan burin nawa bansan adadin samarin da na fatattaka ba,sai gashi yanzu wannan mugun a araha ya sameni sidan..
Ido ta sa mata,
“Amma kuna da alaka da Kamal?
Kai ta girgiza da sauri.
“Bamu da wata alaka sai ta nesa.
Murmushi tai ganin yadda take yatsine fuska.
“Amma zan so jin tarihin ku da yadda wannan auran ya kullu Deeja,kin san har yau mamakin ku nake wallahi.
Baki ta ta6e tare da gyara zama.
“Kamal fa mu karu yake zaune a gidan mu,Abban mu ne ya rike shi tun zamanin yana shekara 10 yazo Kano,Baban shi abokin Abban ne,sai shegen auri sakin bala’i kin san dai mutumin kauye..
“Tare toh su ka taso da yayuna maza dan ni kad’ai ce mace sai yaran riko yanzu gun Mamy.
“Allah ya gani tun tashina jini na bai ta6a gamuwa da shi,gashi shi yafi kowa sanin wani halina da koh a gida basu sani ba,dan fa kusan duk a idonshi ya wakana..
Shiru tai jin ta kwafsa,dan haka cike da halamar tambaya Maman Ihsan ke kallonta,ya ta iya,ta riga da tayi subutar baki.
“Ban sanki ba,sai had’uwar makotaka, haka kawai naji na aminta dake,shi yasa ma ban boye miki zaman mu ba,dan wallahi ni bana sonshi..
Ido Maman Ihsan din ta zaro,
“Toh wa ki ke so?
Ita ma idon ta sa mata,kamin daga bisani ta girgiza kai.
“Ba kowa,abu d’aya na sani shine *INA DA BURI*,burin da har yau ni banga wanda zai iya cika shi ba…
“Dan tsaya dan Allah..
Shiru tai tana kallon Zee din,
“Meye burin naki? Dan Allah ki sanar ni..
Murmushi tayi tare da sake muskutawa.
“Burina nai auren soyayya,irin soyayyar da nake gani a India da littafan soyayya..
“Irin soyayyar da mijina zai ji ina ma ya bani ranshi dan so..
“Irin soyayyar da kullum zan rika jina a sama,ya zamana ni dai d’an soyayya na aura.
Yadda komai ya wakana ta sanar mata har zuwa aurenta da Kamal da yadda aka fasa da Najib.
Ajiyar zuciya tai tare da furzar da iska tana marairaice fuska.
“Sai dai fa ban samu abinda nake son  ba,dan kusan duk samarin da nai kidahumai ne,ba abinda su ka iya sai bud’e hakori,da naga ba haza zan ma kora da hali,in ka ki abu d’aya zanyi wanda koh a hanya ka ganni bani ba kai..
Zama Maman Ihsan ta gyara,
“Wani abu ne wannan? Allah yasa ba abinda nake tunani bane..
Da ido su ka kafe juna,ita kanta tana kunyar tuno da wautar da ta shuka ita da Najib dan kawai bukatar ranta.
Kai ta sunkuyar tana murza yatsa.
“Ina jin ki..
Kasa ta kara yi da kai tare da fad’in
“Soyayyar minti ne muke yi ni da Najib cousin na,wannan ce kawai in nayi nake rabuwa dasu a cikin ruwan sanyi,toh shine,shine fa…
Shiru tai sake yi tana dan sosa keya ganin yadda zee din ta kafeta da ido.
“Ni fa har ga Allah Maman Ihsan ta karya muke yi,amma Kamal da yasha kamamu yaki yarda a hakan,shine kullum sai nasha gori gunshi..
Kasa tai da kanta tana chunno baki.
Ajiyar zuciya Maman Ihsan din tayi.
“Tab,lalle wannan shine kwamachalar..
Kallota ta danyi da halamun tambaya, dan haka sai ta gyara zama.
“Gaskiya kinyi shirme, babba kuwa..
“Sannan ki gode Allah da Kamal din ya taimake ki baki auri Najib ba shi ya aureki..
Kai ta dago da sauri tare da sakar baki,dan haka sai ta kad’a mata kai.
“Kwarai kuwa,koh kina tunanin duk abinda ku ka shuka ba zaki girbe ba a gaba?
Kir ta kafeta da ido,dan haka sai ta cigaba.
“A fa gareki ne abinda ki kai ki ka d’auka a wasa,amma ga samarinki da kuma Allahnki ba wasa bane,dan Najib ba muharamminki bane,koh hannu ya rike miki zunubi ne babba balle azo ga su runguma..
Kai ta sake sunkuyar wa halamun ta gamsu.
“Ita rayuwar nan yanzu da ki ke kallonta wallahi Deeja samari kiris suke jira ki samu tabo,dan fa ko wani saurayin ne yazo a barshi a kin samu dai dai ke,shin bakya tunanin wani yazo ya fad’i halinki wanda a shine silar rabuwar ku?
Shiru tai mata halamun ba gaskiya.
“Dan haka ni a gani na Kamal taimako yai miki da bai barki da Najib ba dan fa a tsakanin ki dashi ba wani sauran mutunci dan ya gama gogar ki da shafar ki a sunan mafita.
Sosai tai mata fad’a, kuma ta gane kuranta har tai istigifari.
Abu d’aya ne bata yarda ba wai Kamal taimako yai mata,abu d’aya ta sani ya taimake ta ne dan ya taimaki kanshi,dan tafi kowa sanin ketar Kamal da bakar muguntar shi.
Sallama sukai ta fito,a bakin kofa ta tararshi ya bake hanya.
Kallon sama da kasa ta mai ta kautar da kai.
“Da izinin wa ki ka fita?
A yatsine ta kalloshi,
“Ji wani karfin hali,toh kai a wa?
Ido ya sa mata,ya ma rasa amsar bata,dan haka kawai sai ya wuce ciki ta bishi da harara.
Sosai ta kunnoshi,dan haka da yaje d’aukan pillow ya tsaya bisa kanta.
“Ya zama rana ta karshe da zaki sake fita ba tare da izini na ba dama..
Kallon tara saura kwata ta fara mishi,a haka ya iya kama kai da iya fad’a, amma a soyayya an baro shi baya…
“Mtsww.. 
Tsaki ta sau mishi tare da mike wa ta zauna.
“Ka fa daina d’aukar kanka a matsayin miji, wallahi darajar Abba kad’ai ke zaunar ni,da kai baka isa ba wallahi..
Kanshi ya nuno da hannu tare da fad’in
“Ni ki ke wa tsaki?
Da sauri ta ce
“Eh din,dan baka isa ba..
Jim yai yana kallonta baki sake.
“Ban isa ba koh?
Cike da tsiwa ta ce
“Sosai,toh kai a wa?
Kai ya jijjiga tare da hulla pillown da ya d’auka ya nufi bakin kofa.
“Yau kwa zan banbance miki tsakanin tsaki da tsakuwa..
Zumbur ta mike ganin ya dannawa kofa mukulli ya cire,ido ta waro tuno da artabunsu na ranar chan,tabbas in ta sake ya risketa tasan sai wata ba ita Deeja ba,dan haka da azama ta sakko da niyar shiga band’aki ta kulle ya riko hannunta kam.
“Yau zan nuna miki yadda zaki koyi ladabin dole ga ni mijinki na koh kin so koh kin ki..
“A mafarkinka kenan wannan, amma wallahi baka isa ba..
Shiru tai ganin ya sunkumeta sama ba tare da ta shirya ba duk da gabanta na matukar fad’uwa amma hakan bai hanata surfa tsiwa ba.
A gado ya direta tare da riketa kam yana dubenta ta inda ba yadda za ai ta kwace.
“Sosai ban isa ba,ba har yanzu da guntun bakinki ba?
Kuka ta sau mishi ganin tai duk dabara ta kasa motsi..
“Ka isa wallahi, dan Allah kai hak’uri…
Dariya ya sa tare fara abinda yai niya,ganin da gaske yake yasa ta kara jiniyar kukan nata.
“Ki adana hak’urinki,dan yau sunanki ‘Sorry’…
Cizo ta kai mishi yai saurin kauce wa,dan haka da sauri ta ce
“Mugu kawai,wallahi bana ciki da iskanci…
Kai ya dago tare da fad’in
“Ai iskanci kin barshi a baya,yanzu wannan ita ce sunnar ki mai lada in kin sa niya..
Kukan gaske tasa tare da fara roko ta Allah da annabi tana kiran Mamy.
Kamal kam yau tasan namijin duniya ne,dan tun tana da bakin roko da fitsara har cikin nutsuwa yasa tai ladab da kanta halamun ya zurmata da yawa,sai ga nan su Deeja an sau jiki ana kwasar hot messages,da sannu ya sassauta rokon da yai mata ganin ta bada gari tai surrender.
Ku biyo mu.
{SAFHA}.........

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "INA DA BURI kashi na 8"

Post a Comment