*INA DA BURI kashi na 11

*INA DA BURI 11*
FEENAT JAFAR
          &
HAFSA(MMN HANEEP)
     11_Sallamar da sallar tai tare da juyo wa.
“Ya isheki haka..
Ido ta zaro..
“Wa ya fad’a ma sallah na isa? Koh ka manta Nana Aisha cewa tai annabi har kumbura kafafunshi suke dan ibada?
Harara ya sau mata,
“Ji ta agun,kamar wata ta Allah..
Rai ta had’e.
”Mey ka ke nufi?
Banza yai mata tare da komawa ya kwanta ita kuma ta cigaba da jero sallah.
Ganin abin ba na hankali bane yasa ya raja’a a baccinshi.
Juyo wa tai tare da tashi cikin sand’a ta leka shi,ai ta gano take taken shi,anshata jiya,dan haka *Dan ba kara wai haihuwar shege*.
****
Duk yadda yaso ya samu kusanci da ita abin yaci tura,ya yi na Allah,ya yi ba annabi,ya sauke duk wani girmanshi gaban Deeja amma bai jin ya ta6a cin karo da mai taurin kan Deeja,gar da gar take nuna bai isa komai ba,dan haka ba karamin jin haushin kanshi yai ba da har ya iya tona mata sirrin zuciyarshi amma taki amsa.
A ganinshi ya bada kanshi gareta da har ya zamo soko.
Dan haka da bak’inshi ya hau warware cewar shi fa da wasa yake,ta ma daina wani rawar kai.
“Dan fa you’re are not my type..
Baki ta ta6e tare da daga kafad’a
“Daga baya kenan wai anyi sadaka da karuwa,dan soyayyar ka sani kad’ai a baki,amma baka iya ta a aika ce ba..
Murmushi ya yi tare da jijjiga kai kawai ya cigaba da abinda yake,ya sani da tai nisa,nisan da bazata ji kira ba,a ganinshi ta hanya d’aya zasu dai daita da Deeja,dan haka yasa kafar wando d’aya da ita.
Daga ranar ya fara seta kanshi da Deeja,bai sake sakacin sanarta yana sonta ba balle yasa dole ta sau ra’ayinta.
Dan haka yanzu aka dawo takun saka a tsakanin su.
***
Yau gida ya shirya ya ce suje gaisuwa tun bayan tariyarsu.
Sosai tasha fad’a da nasiha gun Mamy da Abba duk zancen d’aya ne,tabi mijinta sau da k’afa, dan haka a cike dam suka dawo gida duk yana hankalce da ita.
Baki a d’ane ta dubenshi ganin ya sakace d’akin tare da zuba mata ido.
“Lafiya kuwa? Kamar wanda ka ke bina bashi irin wannan kallon?
Kai jijjiga tare da murmushin mugunta.
“Bashi kuwa turum,yau kuma zaki sauke shi.
Yawu ta had’iye da sauri ganin ya fara kunce buttons na rigarshi yana murmushin mugunta in yaso mata keta yana karasowa,dan haka tuni ta fara raba ido da tunanin abinyi.
Hanci tai saurin toshe wa tare da k’ak’alo aman karya tana daga mishi hannu.
“Kar ka karaso, amai nake ji..
Tsaye yai tare da sa mata ido,da gudu tai hanyar band’aki tana k’ak’arin aman karya ta barshi baki sake.
Chan dai ta fito tana yatsine fuska,
“Zuciyata ke tashi in kana kusanto ni kamar nai amai..
Galala yake dubanta kamin daga 
“Mey ki ke nufi kenan?
Zama tai a bakin gado tana dan cije le6e..
“Wash Allah cikina,anya kuwa ba ciki gareni ba?
Ido ya zuba mata baki sake ganin zata raina mishi hankali.
“A sati biyu dama ciki yake baiyana ‘yar fama?
Rai ta had’e tare da kalloshi..
“Toh mey ka ke nufi? Karyar ciki zan maka komai? Kasan dai zanfi kowa bak’in cikin ace ina da ciki da kai..
Tsam yai yana tunani,so yake ya gaskanta amma ya kasa,sannan ya kasa karyata ta.
Baki ya ta6e,
“Allah raba lafiya,amma ba shi zai hana ki sauke bashin da ki ka d’auka ba..
Zirif ta mike tare da d’ane wa kan gadon ganin dabararta batai ba.
“Wane irin mugu ne wai kai? Na ce ma ban son ka rika kusanto ni zanyi amai..
Gadon ya d’ane tare da janyo hannunta ta fad’o kusa dashi.
“Karya ki ke yi,kuma wallahi sai kin amsa..
Kokawa suka fara sosai,amma dake ya gama gano lagonta da sannu ta bada kai bori ya hau,komai na lafawa ta hau kukan ya cuceta yai mata keta.
Harara ya sau mata lokacin da ya fito a bayan gida har lokacin tana kuka.
“Ki ma ware yarinya ki amsa da lada in kin sanya niya,ni bana ciki da kinibibin karya.
Jiniyar kukan ta kara yana tayata, dan haka sai ta hau hullo mishi pillow yana mata dariyar keta.
Washegari weekend ta kama,ba kero ba gas,dan haka dole ya d’au flaks dan koh motsi taki yi ta tafi gun mai shayin kwanar gidan da jarka a hannu.
Mai barkwanci ne sosai mai shayin, saurayi ne,amma tuzuru,auren ne bai da wuri ba.
Sosai sukai sabo dan a gunshi yake siyan biredi.
Dariyar keta yai ta mishi wai mey zai da flaks? Hala dan kuturin ya motsa?
Kai ya jijjiga yana murmushi
“Za fa kai auren nan ne,za ka gane komai yanzu koh na fad’a ma ba gane wa za kai ba.
Kai ya jijjiga yana zuba mai tea,har da su kwai ya dawo,Allah ya bashi Deeja sai dai ya gode.
Karfi da yaji ta tsiri mishi laulayin karya kawai dan ta wahalarshi.
Haka zai shiga kitchen ya zage yai mata girki wai wari kitchen din yake,haka zai dafo ya kawo mata.
Sai ya kauce tai ta dariyar keta.
Bawan Allah tun baya yarda har ya yarda da gaske ciki gareta,sai dai iskancin Deejan ya fara over.
Karfe takwas na dare yana zaune ta fito a d’aki tana yatsina fuska.
Da harara ya sau mata tare da d’auke kai yana sauya tasha.
Baki ta turo tare da ja ta tsaya a gefe.
“Ni fa d’an wake nake son ci,shi nake marmari..yanzu.
Kai ya dago tare da zuba mata ido,a gaskiya Deeja bakar muguwa ce,yanzu ya gama wanke-wanke bayan yai mata girki taci ta hantse.
Dan haka cike da hatsala ya ce
“Koh kinfi uwa yata mayya yau baki isa na sake shiga kitchen ba Wallahi kinji na rantse…
Juyo wa tai tare da had’e rai,
“Ba sai ka rantse ba,dan nima d’an cikin nawa d’an waken waje yake so na siyar wa ba naka ba,in ba zaka siyo ba sai na fita da kaina..
Jim yai yana k’are mata kallo,ganin yaki tashi yasa ta sau kukan karya tana buga k’afa,kwafa ya yi tare da tashi ya shiga kitchen ya d’akko flaks.
Harara ya dalla mata tare da d’aukan torchlight ya fita yana jijjiga kai,lalle dole ya d’au mataki dan gano shin cikin gaske ne koh kuwa karya?.
Dariya take harda rike ciki bayan ya fuce,harda y’ar kwallar mugunta.
Gabar ya kalla ya kalli yamma,ya ma rasa ina zai dosa?
Mai shayi ne ya fad’o mishi,dan haka kawai sai ya kad’a kai tare da nufar wajen.
SAFHA…


SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "*INA DA BURI kashi na 11"

Post a Comment