INA DA BURI kashi na 4

*INA DA BURI 4*
FEENAT JAFAR
          &
MMN HANEEP
4_Mamy ce ta shigo dan duba koh ta farka taji kukanta da Allah ya isan da take surfa ma Kamal.
Dariyar ya kunshe tare da gyara tsayuwa jin bud’e kofar.
Da harara Mamy ta bita,dan haka sai ta daina Allah ya isan ta hau kuka iya karfinta.
Fita yai ya basu guri, dan haka sai Mamyn ta sa mata ido cike da tuhuma.
“Kina nufin wai mijinki ki ke wa Allah ya isa?
Kukanta kawai take baji ba gani,dan haka kai kawai Mamyn ta jijjiga tare da fad’in
“Ya miki kyau. 
Fita itama yi,ba daban kanta dake sarawa ba da ba abinda zai zaunarta asibitin nan.
Tare da likita su ka dawo sai harara take sau mishi,ganin haka yasa likita ya kalloshi tare da fad’in 
“Mey aka mata ne?
Kallota ya yi duk yau d’aya ta fita a kamaninta.
“Ai da surutai ta tashi ne likita ni da na ma zata koh ta…
“A’a ka manta da hauka na tashi,mugu kawai,wallahi bullukututu dan bazan ta6a yafe maka ba har sai ka sakeni..
Kuka ta sake sawa baji ba gani dan haka ido kawai su ka sa mata.
Rokon Allah da annabi ta rika yiwa Abba akan auren nan ya raba in har yana sonta,ita a bata kowa ta yarda har Najib da dai a had’ata da Kamal.
Lallashinta ya rika yi da fad’in toh,tai hak’uri a koma gida sai ai batun,karshe sai da aka mata allurar bacci ta bar kowa ya sarara.
Washegari fur taki zaman asibitin a dole su ka sallameta,burinta kawai taje gida ayita ta kare.
****
Duk ta dawo kalar tausayi ganin babu sarki sai Allah,dan karan nan sosai Abba ya d’auke mata wuta,ga kyara gun Mamy,ga ketaka ta gun Kamal,bata da sauran dabara a yanzu dan koh Muneera Mamy ta dakatar ta da zuwa.
Kamar wanda aka tsikara ta mike zaune tare da kallon agogo.
Waya ta d’auka tare da danna kiran Najib.
Tsaki tai jin bai daga ba ta sake buga wa.
“Meye kuma?
Fuska ta marairaice kamar yana kallonta.
“Haba d’an uwana yanzu yau sati ina a bala’i amma koh ka kira balle kaji ya na kare?
Zurmashi ta rika yi kamar yadda tasan Najib kam akanta wawa ne har ya zirmu ya sakko.
“Yanzu ya ki ke so ayi toh?
Zama ta gyara tare da sanarshi taimakon da zai mata in dai har zata rabu da auren nan.
Gyale ta dakko tare da fito wa tana leke kamar munafuka, koma wa yai ganin tana sand’a lokacin da ya fito a kitchen da gorar ruwa a hannu.
Ruwan ya ajiye tare da binta ganin ta fice.
A tsaye suke ita da Najib din a bayan gida duk ya dawo wani soko a gabanta.
“A’a Najib,ka yarda dani karan nan in har ka taimakeni toh da wannan kaddarar auren gwara naka ka yarda da dan…
‘Yar dariyar da su ka ji a bayan su ne yasa tai shiru tare da juya wa.
Kallonsu yake had’i da dan jijjiga kai yana yar dariya jin yadda take raina wa Najib d’in hankali.
Harara ta sau mishi tare da juya wa ga Najib.
Murmushi Kamal din ya yi tare da kad’a kai,
“Bana tunanin na ta6a gamuwa dirinka ba sam Najib wanda karamar kwanyar mace ke badda tunaninshi 6at cikin lokaci kad’an..
Juyo wa sukai fuskar Najib din d’auke da mamaki.
“Mey ka ke nufi? 
Deeja ya kallo tare yana murmushi,har mamaki yake yadda ta d’auki sa6a Allah a matsayin hanya mai 6ellewa a gareta,wannan mummunar dabi’ar tana d’aya daga cikin abinda yasa bai shiri da ita koh kad’an.
“Amma Deeja bakya tsoron Allah fa..
Ido ta zaro da sauri tare da bud’e baki.
Kai ya jijjiga.
“Da kina tsoron Allah da kin sanarshi cewa da kanki ki ka bada kwangilar rushe aureku saboda shima baya daga cikin burin ki wanda nasan shima yasan da haka..
Kallo Najib din ta danyi a sace,shima idon ya zuba mata kir dan gaskata gaskiyar lamari.
Sam bata iya karya ba musamman in an mata kamun kazar kuku irin haka,dan haka tuni ta hau mishi kame-kame yai saurin daga mata hannu.
“Ba ki da abin fad’i Malama, dan sai yanzu na sake tabbatar da ba karamin rainan tunani ki kai ba tun da..
Da sauri ta katseshi da fad’in
“Kadan ba karya bane..
“Dallah rufe min baki..
Baki sake take kallonshi da mamaki,wai yau ita Najib ke hantara bata da ta cewa.
“Wato bani da amfani sai in bukatar korar samarinki tazo koh?
Shiru tai ba bakin magana,dan haka tuni ya hau huce haushin shi kanta Kamal na gefe yana kallo jin yadda yake zazzageta gabanshi had’i da tonan silili.
Da kallo ta bishi baki sake har ya 6acewa ganinta ba bakin magana.
Kamal din ta kallo tamkar ta d’aura hannu bisa kai ta sau ihu koh ta shake shi ta huta.
Kafad’a ya daga mata tare da juya wa ya batta nan tsaye baki sake.
Koh ba komai ya toshe wannan 6arnar da ya jima tana kona ranshi ta tsakanin Najib da Deeja.
Ido ya rufe lokacin da yake tuno shan mintin nasu na karya da wai su ka d’auka abin dogwaro duk da su na cin nasara.
Abu d’aya su ka kasa gane wa,shine sa6on Allah sa6on Allah ne duk kuwa da K’ank’antar sa6on toh ya zama zunubi.
Iskar bak’inshi ya furzar tare da zama gefen katifa,fatanshi yasa daga wannan sun rabu kenan.
A fili ya furta zanyi maganinki!
*****
Ganin kunci yana neman hallaka ta yasata futowa falo inda take jiyo hirar su mariya da sauran yaran yan uwa da Abba ke rikon su, Sakina da Maryam sai Mariya datafi kowa kaudi a cikin su,.
Suna ganin ta suka saki murna don dama suna cikin damuwa ganin ta cikin kunci taki kula kowa sunai mata magana ta hausu da masifa, yanzu kuwa da suka ganta cikin walwala har rige-rige rikota sukai cike da murna suna karai mata sannu da jiki,
Nan ta sake cikin su suna hira shakiyancinsu harya fara batar mata da damuwar ta, Mamy data leko ta gansu haka saita bisu da murmushi taji dadin ganin yanda tasoma sakin jiki sakamakon kwanakin baya da take yini a d’aki cike da kunci da damuwa.
Shigowar sa falon ce sanadin dakushewar farin cikin ta,
Shikuwa ko kallon inda take baiba illah sabon darasin hira da suka bud’e da yaran yawan cin hirar tasu akan ‘yan matan yanzu ne, jin an tab’o inda ke masa k’aik’ayi yasashi gyara zama don ganin yasamu damar goga mata zana.,
Saida yakai lomar Abinci bakin sa” kuna jina? Wasu fa ‘yan matan na yanzu ba gwara garin kwaki da suba, a arha b’agas ake tafiya dasu kuni wacce igiyar soyayyata ta zargomin ko naira hamsin kabata kana iya sumbatar kuncin ta ko fiye da haka ke alakoro ma inta yaba murmushin ka saita baka ka tsotsa”,
Dif! Sukai danjin yanda akalar zancen nasa ya dosa duk da basu fahimci ainihin meyake nufi ba sunsan dai da Deeja yake, don haka sukai kallon kallo a tsakanin su sukai dariya tareda canja akalar zancen.
Deeja kuwa? Jitai marar ta takulle hankalin ta yatashi shikad’ai yajiyo sautin da cikin ta yabada kullllll!! Alamun tsurewa da batun sa,
Don haka ya gumtse dariya ganin duk ta firgice tayi narai- narai da ido tamkar tasaki kuka don tasan Kamal zai iya tona asirinta gurin k’annan ta don kirki bai isheshi ba,
Duk da ya kunshe dariyar sa saida takai da kubucewa don ganin tamike tsam tana b’arin shigewa band’aki da gudu.
*****
Cikin wannan kwanaki ya hana kansa sukuni a sakamakon abinda yayi mata rannan a gaban su Sakina, don haka yafaki idon mamy dake kicin ya fad’a mata d’aki ya maida kofa yarufe.,
Zunbur tamike a razane don bata tab’a tsammatar zai bankado mata d’aki cikin irin wannan lokacin.,
Ganin ta taso masa yasashi dakatar da ita,
“Kinga karki tareni da hayagaga Abu d’aya zuwa biyu yakawoni gareki,
Yafara magana cikin tausasa murya.,
“Na farko naga kwana biyu kina boye kanki a d’aki bayan naga rannan kece harda zaman hira a falo shine nazo naji ko lafiya?
” sannan kuma intayaki jajen Abinda yafaru”,
Shuru yai yana saurarar cewar ta,
Shuru ta shareshi, ya tsira mata ido da kyau yana nazarin ta, ta rame sosai damuwarta na tasowa ne tun daga tsakiyar zuciyar ta a lurar da yayi mata kenan, yajima bai mata irin wannan kallon kurillar ba yanzu sai yaji miliyoyin sonta na tasomasa muryar ta kawai yake da muradin ji gashi kuma taki magana,,
Ya sake gyara tsayuwa yanai mata dariyar tura haushi,,
“Au na manta naga kwana biyu kun bata da me debe miki kewa ni kuma dazan debe miki ta ainihin kin nunan iyaka ta”
A kufule tace”
“Burinka yacika to yanzuma zaman nan da nake ubangiji nake kaiwa k’rarka kuma gashi tun ba’aje ko inaba yasomai min sakayya”
“Amma yakamata ace cikin kunya kikayi maganar nan”
Duban rashin fahimta taimasa,,
“Yanzu duk rashin tsarkin ki bakiji kunyar gurfana gabansa kina kai karar mutumin kirki irina? Ko bakya tuna abinda kukai da Najib?
Ta kasa magana,,
“Da kinada hankali da tunani jinjina ya kamata kimin dana taimake ki na aure ki donni naganki yakai sau dari a yanayin dabai dace ba tare da Najib,,
“Amma bantaba fasa sonki ba Deeja, kinga shi Aminu gani d’aya yayi miki kuna asha ruwan tsintsaye ya zargawa Karen sa igiya to kice da yaga Najib sakale da kugun ki yana kokarin zira miki harshe a baki had’iyar zuciya zaiyi ya mutu”
Ba shiri tamik’e zaune cikin haki tana waige-waigen don tsoron kar wani yajiyo su,,
Kamar zata rushe da kuka tace” kai Kamal kaji tsoron Allah yaushe kaga Najib sakale da k’uguna?
“Kina nufin sak’ale k’ugu baikai tsoma harshe cikin baki bane?to ai naga abinda yafi haka ma kuma ko agaban wanene zan bada shaida”
Kofa tanuna masa cikin tunzura, “tafi bayan duniya kabada shaida”
“Aiba saikin sani ba ko rakiya kika gayyace ni lokacin da kuke sheka ayar ku?.
“Ni yanzu Alfarma nazo nema tunda Najib yagudu nasan kina cikin damuwa don haka ki taimaka kibani dama na maye gurbin Najib duk Abinda kike zaton ya iya dama wanda kike bukata babu wanda ban iyaba har karima sai kinsamu”.
Hawaye tasoma tana marmasa ido tsoro fal ranta,
“Kamal Dan Allah kafuta kabani guri inhar ka gwada kanason tarewar mu Allah ya isa ban yafe ba haka inka kuma shigo min d’aki,,
Yana dariya ya amsa,,
“Allah ya isar shigowa daki kawai zan guda amma maganar tariya banida matsala inhar zan dinga zagayowa koke ki faki ido kuzo tomu shekara a hakan”
Zuwa yanzu tafara kuka wiwi,
Duk da yalura kamar numfashin ta zai dauke don kuka da tashin hankali amma bai fasaba,,
Yanzu nazo kinsame ni a b’agas haka zaki barni natafi a bagas? Kibani dama ko d’aya ce Najib bazai nunamin iya shan minti ba donni ma ba baya bane”
Tariga tagama kaiwa karshe don haka ta d’ora hannu a ka ta kwarma uban ihu, tuni kamal ya b’ace,,
Mamy da Abba ne sukai rige rigen shigowa suga wanne hali ‘yarsu tashiga data cika gidan da wannan uban ihun…..,
Tsaki mamy tasaki tai komawar ta kicin cike da takaicin khadeeja,
Shima Abba rufeta dafada yayi kana ya futa yana fadin nasan ”
matakin da zan dauka akanki”
****


SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "INA DA BURI kashi na 4"

Post a Comment