CANJIN YANAYI 2


DAGA ALK’ALAMIN Y’AR MUTAN JEGA
©MARYAM ADAM
           Ganin cewa ta shiga kitchen (madafi) d’in ne ya saka Zainab ta biyo ta daga baya d’in’ “Maman Farha kiyi hak’uri sai yanzu na samu Abban Farha ya sakoni, gashi ko Breakfast (karin safe) ban samu na d’ora ba, sauk’in abin yau weekend (k’arshen sati) ne su Farha na gidan Hajiya”.
“Uhmm”, shi kawai ta samu furtawa ta koma d’akinta ta fasa dafa ruwan tea (shayi) d’in, saboda sanin doka ce daga Abban Farha ba za’a yi mashi girki biyu ba. Amma hak’ik’anin gaskiya ana shiga hakk’nta ita da yaranta, sai dai tunaninta d’aya duk abinda kayi hak’uri watarana zai zamo labari, kuma tasan ranar da duk Zainab ta haihu dole ta rik’a shiga kitchen cikin lokaci. Akan hakan ne yasa ko yaushe bata rabo da d’an lemu da cin-cin ko don yaranta.
*****
Yau kam ta saka ma ranta duk tsiyar Abban Farha sai ta yi wanka a toilet (bayi) d’inshi, saboda haka bayan ta gama girkinta ta yi wanka suka had’u suka ci abinci dukansu har yaran, suna gamawa tayi masu shimfid’a suka kwanta shi ko ya d’an fita Exercise (motsa jiki), sai wuraren 11:00pm sannan ya shigo gidan.
Da fara’arta ta taryeshi sannan ta shiga bayi ta had’a mashi ruwan wanka ya shiga ya fito, saman kujera ya ganta kwance sagale da towel d’inta alamar shi take jira ya fito ita ma ta shiga wankan saboda yanayi na zafi dake addabar mutane.
Murmushi ya sau mata kana ya kautar da kanshi gefe yana mai goge jikinshi, “wai ni Hafsat har sai yaushe ne zaki daina rigimar cewa sai kinyi wanka a bayina?”.
Maganarshi ce ta doki dodon kunnenta da tayi sanadiyyar dawowa a hayyacinta, fuskar ta k’ara had’ewa tamkar hadari ya had’o kayanshi daga gabas.
“Bansan me kake yimin 6oyo abayinka bane da baka so nagani, kuma ina ganin kullum ranar girkina sai nayi ma shara da wankin bayin, amma duk nace zan shiga wanka a cikinshi sai ka nuna min baka so, bayan can farko ba hakan bane saboda da kanka ka koyan hakan na buk’atar nayi wanka a bayinka wanda wani lokaci ma muke yi a tare”.
Tana kai k’arshen maganarta sai ga hawaye suna ambaliya daga fuskarta, wanda ke nuna alamar cewa abin ba k’aramin zafi yake mata a zuciya ba.
Towel (shawul) d’in ya sagale a k’ofa sannan ya tako gurinta ya zauna a gefenta, hannunta ya rik’o yana wasa da yatsunta had’e da kai masu kiss (Sumba), harara ta sau mashi sannan ta fisge hannun nata daga nashi ta mik’e sagale da shawul d’inta zata bar d’akin.
Saurin taryota yayi yana mai bata baki kamar kullum in har irin wannan rigimar ta taso a tsakaninsu, “haba Maman Farha ki daina damar da kanki kan wannan abin, ina so ne a fahimci cewa yanayi ya canja, kuma na gaya maki cewa lokaci zai wuce”.
“Ni fa in har kana so na fahimceka to ka gayamin me yasa lokacin sanyi ko lokacin yanayin ruwan sama baka hana min wanka a bayinka?”.
“Zan gaya maki amma ba yanzu ba, haba Hafsat ya kamata ki fahimce ni mana, ke kanki kinsan bazan ta6a sauya maki ba har abada, saboda kinsan cewa ke ta dabance har yau har gobe kuma har jibi…..”.
Saurin taryar numfashinshi tayi tana mai d’aga mashi hannu alamar bata ma son cigaba da sauraren kalamanshi, sannan ta furta’ “a da can farko na yarda da way’annan kalamai naka, amma a yanzu jinsu nake yi tamkar d’an koyo ya d’auki sarewa yana busa”.
Dariya yayi sosai har da had’awa da rik’e ciki kana ya furta’ “miye banbancin zamantakewata ta farko dake data yanzu?”.
Wani kallon jin haushi ta bishi dashi wanda ke nuna kalamanshi sun fara ginsar da ita. “Ai ina ga tamkar bayanin a bayyane yake ba sai na wahalarda kaina ba”.
“Amma k’aramin misali, a da can farko ina manne dakai a koyaushe, inyi yanda naso dakai, muyi hira a lokacinda muka so, bani da shamaki da kai, yanzu fa gayamin haka ne?”.
Hannunta ya rik’o ya zaunar da ita saman cinyarshi yana wasa da jelar gashin kanta. “Hafsat ina so ki fahimci cewa har yanzu way’annan abubuwan basu sauya a tsakanina dake ba, amma me yasa yawancin Mata kuke tunanin da miji ya auri wata Mace ya daina son ku?”.
Sai da ta rik’o gabanshi mai nuni da cewa taci kwalarshi ne sannan tace’ “close the chapter (a rufe zancen) in har ba so kake yau mak’ota su shigo k’watarka a hannuna ba, don haushin maganarka nake ji”.
Sai da ta kai k’arshen zancen sannan ta cire hannunta daga kwalarshi data rik’e ta dawo tana wasa da sajenshi daya kwanta lub dashi, cakul_kuli ya rik’a yi mata sai da ta kai k’asa tana dariya.
Tallabota yayi kana ya marairaice yana mai rok’onta data gaya mai CANJIN YANAYIN da take ganin can farko da yanzu ba d’aya bane.
“Ai ko kanada aiki Yalla6ai, sai ranar da ka gayamin dalilinka na korata daga bayinka wanka”.
Ido ya d’an zaro kana ya furta cewa’ “wannan sirrina ne bazai yuyu na sanarda ke ba”.
Cikin damuwa ta zare jikinta daga nashi ta shammaceshi ta fice daga d’akin domin yin wanka su fita waje su kwanta.
Muje zuwa.✍🏻


SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "CANJIN YANAYI 2"

Post a Comment