INA DA BURI kashi na 16

*INA DA BURI*
MARYAM ADAM.
FEENAT JA’AFAR
         &
HAFSA(MAMAN HANIF).
    16_Glass din motar ta kwankwasa ganin ya jingina kanshi a jikin motar,a hankali ya zuge tare da kallonta yana k’ak’alo murmushi.
“Dan Allah kai hak’uri, nasan wataran zata daina.
Murmushi ya yi tare da kad’a kai,da ace Deeja na da hali irin na Muneera tabbas da yaji dad’in aurenshi.
A kance wai aboki na kwafar halin abokinshi toh tabbas Deeja bata kwafa ba,matuka yana son mace marar hargowa da ladabi had’i ga tarbiya.
Ba daban a gabanshi Deeja ta tashi ba, toh tabbas zai ce ba rainon Mamy ba ce.
“Ba komai Muneera,ba dai har kin fito ba?
Kai ta kad’a,
“Eh tafiya zanyi.
Motar ya bud’e mata tare da fad’in
“Shigo toh na sauke ki,dan hanyar gidan zanyi.
Jim tai tare da kad’a kai ta zaga bangaren da ya bud’e mata su na tafe su na tad’in Deejan.
Sai chan dare kusan goma ya shigo,lokacin tana zaune a parlour ta cika ta 6atse.
Koh ta kanta bai bi ba ya shige d’aki bai da walwala shima.
Tun daga ranar ya sauya mata,zai wuya taga fara’ar shi kullum a dunkume, baki ta ta6e,a ganinta wai tafi nono fari.
Kusan wata guda bai shiga sabgarta,iyakarshi da ita ido,in ta ga dama ta bashi abinci yaci,in abin ya motsa ta hana shi,dan haka shiga kitchen bai mishi wahala ya girka yaci ya fuce.
****
Tsam tai a band’aki tana wanka tare da saka kunne ta kofar band’akin jin yana dariya kasa-kasa.
“Oh no dorling, believe me,a satin nan kad’ai kin sanya na zurmada yawa…
Shiru yai halamun saurare,chan taji ya sake wata munafukar dariya cikin wani salo na so tare da fad’in
“I tell you..
Dariya ya sake yi,
“Ok,bari na duba zuwa gobe,Insha-Allah ki share min hanya…
A masife ta bud’e kofar band’akin ta fito tana huci daga ita sai towel.
Ido ya sa mata yana murmushi halamun yana sauraren ta wayar.
“Baby bani minti biyu zan kira..
Dariya ya danyi tare da kashe wayar yaci kunu kamar bashi yanzu yake dariya ba.
“Ni fa wallahi bazan d’au wannan wulakancin ba da rainin hankali,ban hanaka waya da koma wacce shegiyar bace amma ka yi a waje,banda cikin d’akina kuma bisa kan gadona…
Ido ya sa mata ganin wani karfin hali wai *Sadaka da d’an kishiya*.
“Ke a wa toh?
K’ugu ta kama tare da fad’in
“Oho,ni dai na fad’a maka,na daga ma k’afa amma naga abin sai gaba yake sake yi,ban hanaka ba,balle ka ce kishin ka nake,amma kai a waje.
Magana zai yi sai yai shiru tare da duba waya jin sako ya shigo,bud’ewa yai.
A hankali fuskarshi ta washe da murmushi.
Tuni ya sauka a gadon tare da fita yana reply ga text din da ya shigo ya batta nan tsaye.
Da harara ta bishi tare da ta6e baki.
Wannan dabi’a da Kamal ya koyo ta waya da budurwa ba karamin ci mata tuwo a kwarya take ba,tabbas ba kishi take ba,a’a, bakin cikinta d’aya da ita bai rabu da ita ta samo mai sonta da mutuwa a kanta ba kamar yadda taci buri.
Kwafa tai tare da k’arkad’e shimfid’a,dole yau ayita ta kare,sam bazata sa6u ba wai bindiga a ruwa,yau dole ya san yadda zai da ita.
Bargo taja jin an fara ruwa amma yana chan parlour har ta gaji da jiranshi.
Da harara ta bishi tare da d’auke kai,hararar shima ya bita dashi tare da ajiye wayar yana cire kayanshi,wanka ya shige bai bi koh ta kanta ba.
Bargon ta yaye tare da tashi ta d’au wayar ta shiga cikin chart nasun wanda network ya d’auke dole suka hak’ura ya dawo d’aki.
Tsaki taja ganin yadda yake zuba mata kalami tamkar wani na gaske budurwar na aiko mishi da kiss,maganar turo magabata yake network din ya d’auke.
Wayar ta ajiye jin zai fito tana aika mishi harara.
Jiki ya goge da towel yana yar waka irinta masoya.
“Bari kaji da wai,wannan ba shi zai sauya min Buri ba,wallahi in kaso ka auro hud’u amma in na fuce,dan fa dole ka sallameni nima na samo nawa masoyin..
Towel din ya ajiye yana jinta tare da fesa body spray yana murmushi.
Juyo wa yai daga shi sai wandon ball iya gwiwa tare da hayo wa gadon yana kallonta wani iri.
Bargo yaja yai mata banza,dan haka tuni ta kara kulewa ta hau bala’i wanda ya jima baijishi ba.
Tashi yai tare da zama ya jingina pillow ya sata a gaba kamar TV.
Bakin ya kalla sam koh coma batai balle ta sanya full stop a masifar duk rabi akan sai fa ya sallameta itama ta samo saurayinta mai sonta.
Bak’in yai saurin toshe wa da nashi tare da janyota gareshi ya kashe maganar.
Yau kam a gaske ya tura ta bango,dan haka dakyar ya saito da tuaninta ta sauke taurin kai tare bin ra’ayin zuciyarta kamin tai surrender.
Yafi kowa sanin alkibilar da Deeja dosa,dan haka cikin ruwan sanyi yake kashe bakin tsanyar.
Kuka take mishi tsakaninta da Allah bayan komai ya lafa, kam ya riketa yaki sakarta, dan haka cikin sassanyar iskar daminar had’i da sanyin ruwan dake busowa bacci yai awun gaba da ita a haka tana mitar ya cuceta.
Kai ya girgiza yana murmushi, bai jin zai iya rabuwa da Deeja duk rintsi kuwa,amma hakan bazai hana ya samu saukin rayuwa ba,dan haka ya riga da ya gama shawarar abin yi duk kuwa da yasan zai sa Deejan a tsaka mai wuya.
Dan haka akanta bazai hana zuciyarshi abinda tai niya ba koh da kuwa gangar jikinshi bata so.
Bakin yaja kad’an tare da fad’in
“Ni da ke ai takalmin kaza ne,in an mutu sai a raba, ki shirya kar6an haka.
Bargo yaja musu tare da gyara kwanciya yana jin saukar ajiyar zuciyarta.
Kai ya girgiza, a kullum ana kirarin ba’a sonshi amma hakan bai ki a lafe mishi jiki ba koh da kuwa ya sauta, matuka yana mamakin kalar rigima irinta Deejan shi.
Hannu ya kai tare da dungure mata kai a hankali yana dariya,cikin baccin ta chunno baki tare da dan motsa wa, kai ya kad’a, yanzu ya yarda a jininta abin yake.
SAFHA…✍🏾


SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "INA DA BURI kashi na 16"

Post a Comment