INA DA BURI kashi na 9
*INA DA BURI 9*
FEENAT JAFAR
SDY JEGAL
SDY JEGAL
&
HAFSAT(MAMAN HANIF)
*Na gaida mutanen kirki ma’abota sada zumunci, princess Hassy, Autar Hajiya, FIdo sodangi, Sadiya Stylish, Allah yasaka da Alkairi ykr dankon zumunci AMEEN*
9
Yanayin da ya fuskanci ta shiga ne yasa wani b’angare na zuciyarsa ya soma k’aryata d’ayan sashen dake tunatar dashi k’iyayyar da Deeja ke masa.
Cikin k’warewa da son nuna mata k’warewarsa ya shiga sarrafa Deeja, wacce tunda tayi surrender ta shiga kokawa da zuciyar ta wacce ta soma k’ayatuwa da sak’onnin da Kamal yaso aika mata. Duk yanda taso ta kame kanta don gudun gori irinna Kamal amma ta kasa, a dole ta biye masa don ta kasa sarrafa kanta ji take ma tamkar ba ita bace, a yayin da Kamal ya sabunta mata duniyarta gaba d’aya.
Cikin nishad’i da matuk’ar farin ciki yake jin kansa, Kalmar hamdala ke wanzuwa cikin bakinsa tare da nanata “Ina sonki Khadeeja”. Cikin wannan yanayin mai cike da d’unbun dad’i da farin ciki ya raya darensa, wanda farin cikin ya k’ara armashine a yayin da ya samu tabbacin a iya shan mintin da suke ambata Najib ya tsaya, don haka ya k’ara d’aga darajarta ya kuma k’ara marta bata, wanda ko iya nan ya tsaya ya san baiyi zab’en tumin dare ba.
*Asuba ta gari*
Garin ya waye masa da Alkairi don wata nutsuwa yaji tana shigarsa yanajin tamkar dala da gwauran dutse ya sauke saman kansa.
Tun dawowar sa daga masallaci ya soma jiyo sautin kukanta, nan yayi turus yana kallonta, miliyoyin k’aunarta na k’ara nunkuwa cikin ransa, cikin wannan kukan bacci ya sure ta a daren jiya, gashi yanzu ma dashi ta farka, don haka ya shanye mamakinsa ya k’arasa cikin d’akin ya zauna yana saurarar kukanta wanda yai masa kama dana nadama koma kai tsaye yace na k’iyayya, duk da ya soma k’aryata wannan batun a daren jiya.
Kuka take sharb’a k’wakk’waran motsi ta kasa yi, ci kanki Kamal bai ce mata ba shi bai San dame zaiji ba, da farin ciki daya cika ransa koda rarrashin da yasan ko ya yi ba gwaninta zai mata ba? Koda murnar bata fad’a tarkonda ta shiryawa kanta ba?.
Tayi kukan ya isheta har ta sami sarari a zuciyarta, Allah ya isa kuwa babu kalar wacce batayiwa kanta ba, kuma taji kullacin tana kuka bai rarrasheta ba, bayan yasan tana buk’atar rarrashin yayi biris da ita.
Sai da ya tabbatar ta tsagaita kukanta sannan ya taso ya zauna gefenta tare da kamo hannunta ya shiga murzawa, maimakon yayi rarrashin ko yayi banbaki a’a sai ya jefeta da bak’ar magana.
“Yanzu mun zama d’aya ko? Ya juyo da fuskarta sosai suna fuskantar juna ya shiga zagaye fuskarta da yatsansa yana faman murmushi.
Bai sake tanka mata ba, kuma bai damu da sai ta bud’e idonta data rintse ba. Haka yake kalle fuskarta tare da shafa duk inda yaso a fuskarta k’aunarta na fizgar sa.
Maimakon ya fad’i kalmarda za ta sa mata nutsuwa ko su fallasa mata sirrin zuciyar sa sai ya kuma kunno ta.
“Wai me yasa ba zaki bud’e ido ki kalleni sosai ba, ko kunyata kike ji ne? ni ne fa Kamal wanda ban isaba waye ni da zaki ji kunya ko mamaki kike?.
Hakanan taji tanason kecewa da kuka don takaici da k’uncin da Kamal ya haddasa mata ga bak’ak’en maganganunsa, har wani murmushin mugunta yake mata don dai kawai ya nuna mata yaci moriyar ganga….
Don haka ta daddage k’arfin da ya rage mata ta tureshi tayi wurgi da bargon, aguje ta nufi band’akin tana gurshek’en kuka, ya bita da kallo yana dariya.
Taji dan sanyi data futo daga wankan taga d’akin a gyare hatta kayan baccinta daya dinga watsi dasu ya tsince su d’akin sai k’amshi yake.
Cikin shirin futa aiki ya shigo fuskar sa d’auke da murmushi yake duban ta harda kashe mata ido a yayin da ya matso daf da ita yakamo hannun ta ya manna mata Sumba wacce hatta yan cikin ta saida ya amsa.
Don haka ta nemi nutsuwarta ta rasa kawai sai tayi zaman d’abaro a bakin gado tana maida numfashi to baki ya mutu muruss.
cikin tattausan lafazi ya furta’ “Ina sonki, zanta sonki Khadeeja tun a daren jiya na k’udiri a niyar bautawa soyayyarki, ina so ki nutsu ki kwantar da hankalinki ki bani dama, ni nayi alk’awarin zan jagoranci cikar burin ki”.
Ya d’anyi shuru don saurarar cewarta, tayi shuru don batada abin cewa.
“Ina Neman Alfarma a gunki Deeja ki sanya mafarkina ya zama gaskiya, a daren jiya naga wani abu tare dake me kama da k’wayar sonda nake nema a gunki don Allah karki k’aryata mafarkina”.
Anan ne tasamu damar tofawa, “in dai Abinda nake ji a k’irjina na bana son zama dakai a matsayin miji ba k’iyayya bace to a gaskiya bansan kaina ba”.
Tana kai aya ya amshe, “Haka kika tab’a ganin aurenk’i? Haka kika tab’a ganin amarya bata tab’a yaji ba? Haka kika saba ganin auren k’i amarya da ango a daren farko sun raya daren salim alim tamkar wanda sukai auren soyaiya?, duk tambayarki nake yi haka kika saba gani?”.
Kunya, haushi, takaici duk ya hade mata, koma me zaice mata ita ta bada kanta daya zo da buk’ata ta biye masa har yayi galaba akanta cikin dad’in rai.
Kamar yasan abinda take rayawa a ranta, yace’ “ba kece da zuciyarki ba ba kece da gangar jikinki ba bare in nazo da buk’ata ki bijiremin, amma ko yaya so da k’i suna nuna kansu in an kasance tare”.
A zuci ta raya, yi ka gama cimun fuska kawai ka kauce”.
Siraran hawaye ne ya shiga sirnano mata bai bata damar magana ba yaci gaba.
“Ina sonki kuma zan cigaba da sonki ko yaushe, ki kwantar da hankalinki ki kori duk wata damuwa ki kwanta kiyi bacci mai dad’i a cikinsa kid’an bud’amin waje kad’an a zuciyarki da nuna so na samu na shigo, ta hakanne zamu samarwa iyayenmu farin cikin da suka zata daga garemu”.
Ya kai hannunta leb’ensa ya sunbata cikin gwaninta sannan ya saki hannun yana cewa’ “zan futa amma yinin yau aikin da na baki shine, ki lalubi zuciyarki kiji in akwai guntun sona koda jariri ne don Allah inna dawo ki sanar dani, ni nasan yanda zan raini abina ya girma”.
Wannan yad’an bata nutsuwa ta d’an rage cin magani ta kuma rage hawaye. Sai dai har wannan lokacin baiji furucinta ba.
*Na gaida mutanen kirki ma’abota sada zumunci, princess Hassy, Autar Hajiya, FIdo sodangi, Sadiya Stylish, Allah yasaka da Alkairi ykr dankon zumunci AMEEN*
9
Yanayin da ya fuskanci ta shiga ne yasa wani b’angare na zuciyarsa ya soma k’aryata d’ayan sashen dake tunatar dashi k’iyayyar da Deeja ke masa.
Cikin k’warewa da son nuna mata k’warewarsa ya shiga sarrafa Deeja, wacce tunda tayi surrender ta shiga kokawa da zuciyar ta wacce ta soma k’ayatuwa da sak’onnin da Kamal yaso aika mata. Duk yanda taso ta kame kanta don gudun gori irinna Kamal amma ta kasa, a dole ta biye masa don ta kasa sarrafa kanta ji take ma tamkar ba ita bace, a yayin da Kamal ya sabunta mata duniyarta gaba d’aya.
Cikin nishad’i da matuk’ar farin ciki yake jin kansa, Kalmar hamdala ke wanzuwa cikin bakinsa tare da nanata “Ina sonki Khadeeja”. Cikin wannan yanayin mai cike da d’unbun dad’i da farin ciki ya raya darensa, wanda farin cikin ya k’ara armashine a yayin da ya samu tabbacin a iya shan mintin da suke ambata Najib ya tsaya, don haka ya k’ara d’aga darajarta ya kuma k’ara marta bata, wanda ko iya nan ya tsaya ya san baiyi zab’en tumin dare ba.
*Asuba ta gari*
Garin ya waye masa da Alkairi don wata nutsuwa yaji tana shigarsa yanajin tamkar dala da gwauran dutse ya sauke saman kansa.
Tun dawowar sa daga masallaci ya soma jiyo sautin kukanta, nan yayi turus yana kallonta, miliyoyin k’aunarta na k’ara nunkuwa cikin ransa, cikin wannan kukan bacci ya sure ta a daren jiya, gashi yanzu ma dashi ta farka, don haka ya shanye mamakinsa ya k’arasa cikin d’akin ya zauna yana saurarar kukanta wanda yai masa kama dana nadama koma kai tsaye yace na k’iyayya, duk da ya soma k’aryata wannan batun a daren jiya.
Kuka take sharb’a k’wakk’waran motsi ta kasa yi, ci kanki Kamal bai ce mata ba shi bai San dame zaiji ba, da farin ciki daya cika ransa koda rarrashin da yasan ko ya yi ba gwaninta zai mata ba? Koda murnar bata fad’a tarkonda ta shiryawa kanta ba?.
Tayi kukan ya isheta har ta sami sarari a zuciyarta, Allah ya isa kuwa babu kalar wacce batayiwa kanta ba, kuma taji kullacin tana kuka bai rarrasheta ba, bayan yasan tana buk’atar rarrashin yayi biris da ita.
Sai da ya tabbatar ta tsagaita kukanta sannan ya taso ya zauna gefenta tare da kamo hannunta ya shiga murzawa, maimakon yayi rarrashin ko yayi banbaki a’a sai ya jefeta da bak’ar magana.
“Yanzu mun zama d’aya ko? Ya juyo da fuskarta sosai suna fuskantar juna ya shiga zagaye fuskarta da yatsansa yana faman murmushi.
Bai sake tanka mata ba, kuma bai damu da sai ta bud’e idonta data rintse ba. Haka yake kalle fuskarta tare da shafa duk inda yaso a fuskarta k’aunarta na fizgar sa.
Maimakon ya fad’i kalmarda za ta sa mata nutsuwa ko su fallasa mata sirrin zuciyar sa sai ya kuma kunno ta.
“Wai me yasa ba zaki bud’e ido ki kalleni sosai ba, ko kunyata kike ji ne? ni ne fa Kamal wanda ban isaba waye ni da zaki ji kunya ko mamaki kike?.
Hakanan taji tanason kecewa da kuka don takaici da k’uncin da Kamal ya haddasa mata ga bak’ak’en maganganunsa, har wani murmushin mugunta yake mata don dai kawai ya nuna mata yaci moriyar ganga….
Don haka ta daddage k’arfin da ya rage mata ta tureshi tayi wurgi da bargon, aguje ta nufi band’akin tana gurshek’en kuka, ya bita da kallo yana dariya.
Taji dan sanyi data futo daga wankan taga d’akin a gyare hatta kayan baccinta daya dinga watsi dasu ya tsince su d’akin sai k’amshi yake.
Cikin shirin futa aiki ya shigo fuskar sa d’auke da murmushi yake duban ta harda kashe mata ido a yayin da ya matso daf da ita yakamo hannun ta ya manna mata Sumba wacce hatta yan cikin ta saida ya amsa.
Don haka ta nemi nutsuwarta ta rasa kawai sai tayi zaman d’abaro a bakin gado tana maida numfashi to baki ya mutu muruss.
cikin tattausan lafazi ya furta’ “Ina sonki, zanta sonki Khadeeja tun a daren jiya na k’udiri a niyar bautawa soyayyarki, ina so ki nutsu ki kwantar da hankalinki ki bani dama, ni nayi alk’awarin zan jagoranci cikar burin ki”.
Ya d’anyi shuru don saurarar cewarta, tayi shuru don batada abin cewa.
“Ina Neman Alfarma a gunki Deeja ki sanya mafarkina ya zama gaskiya, a daren jiya naga wani abu tare dake me kama da k’wayar sonda nake nema a gunki don Allah karki k’aryata mafarkina”.
Anan ne tasamu damar tofawa, “in dai Abinda nake ji a k’irjina na bana son zama dakai a matsayin miji ba k’iyayya bace to a gaskiya bansan kaina ba”.
Tana kai aya ya amshe, “Haka kika tab’a ganin aurenk’i? Haka kika tab’a ganin amarya bata tab’a yaji ba? Haka kika saba ganin auren k’i amarya da ango a daren farko sun raya daren salim alim tamkar wanda sukai auren soyaiya?, duk tambayarki nake yi haka kika saba gani?”.
Kunya, haushi, takaici duk ya hade mata, koma me zaice mata ita ta bada kanta daya zo da buk’ata ta biye masa har yayi galaba akanta cikin dad’in rai.
Kamar yasan abinda take rayawa a ranta, yace’ “ba kece da zuciyarki ba ba kece da gangar jikinki ba bare in nazo da buk’ata ki bijiremin, amma ko yaya so da k’i suna nuna kansu in an kasance tare”.
A zuci ta raya, yi ka gama cimun fuska kawai ka kauce”.
Siraran hawaye ne ya shiga sirnano mata bai bata damar magana ba yaci gaba.
“Ina sonki kuma zan cigaba da sonki ko yaushe, ki kwantar da hankalinki ki kori duk wata damuwa ki kwanta kiyi bacci mai dad’i a cikinsa kid’an bud’amin waje kad’an a zuciyarki da nuna so na samu na shigo, ta hakanne zamu samarwa iyayenmu farin cikin da suka zata daga garemu”.
Ya kai hannunta leb’ensa ya sunbata cikin gwaninta sannan ya saki hannun yana cewa’ “zan futa amma yinin yau aikin da na baki shine, ki lalubi zuciyarki kiji in akwai guntun sona koda jariri ne don Allah inna dawo ki sanar dani, ni nasan yanda zan raini abina ya girma”.
Wannan yad’an bata nutsuwa ta d’an rage cin magani ta kuma rage hawaye. Sai dai har wannan lokacin baiji furucinta ba.
Ya d’au tsawon lokaci
yana zayyano mata bayanin da suke sata jin kunya da kuma jin ba zata yafewa
zuciyarta ba, kafin yai mata sallama yabar gidan.
Nan dai ta zauna ta
kimtsa kanta sannan ta futo falo, nan ma a gyare yake idon ta ya kai kan canter
table wanda ke d’auke da break lafiyayye daya shirya mata, don haka bata tsaya
b’ata lokaci ba ta hau ci don wata mahaukaciyar yunwa take ji, taji dad’in
roman naman kajin da yayi mata wanda yaji kayan had’i tas ta shanye roman ta
bar ragowar naman.
Komawa tai d’aki ta kwanta bayan ta gama break d’in don duk bata jin dad’in jikinta, duk jikinta yayi sanyi ta sawa ranta Kamal ya riga ya gama cutarta dole inya dawo ayita ta k’are.
Cikin wannan zullumin ta yini.
A nasa b’angaren kuwa? Yini yayi cikin nishad’i da begen matarsa don ta shayar dashi mamaki don haka yini yayi yana tunaninta, gangar jikinsa ce a gurin aiki amma hankalinsa na gida, har a gurin aikin abokansa sai da suka fahimci farin cikin da yake ciki, don shi kad’ai yake zuba murmushi a duk sanda ya tuna daren Alfaharinsa.
Karfe hud’u na yamma ya had’o yanasa yanasa yadawo gida don ya kasa aikin kirki.
Komawa tai d’aki ta kwanta bayan ta gama break d’in don duk bata jin dad’in jikinta, duk jikinta yayi sanyi ta sawa ranta Kamal ya riga ya gama cutarta dole inya dawo ayita ta k’are.
Cikin wannan zullumin ta yini.
A nasa b’angaren kuwa? Yini yayi cikin nishad’i da begen matarsa don ta shayar dashi mamaki don haka yini yayi yana tunaninta, gangar jikinsa ce a gurin aiki amma hankalinsa na gida, har a gurin aikin abokansa sai da suka fahimci farin cikin da yake ciki, don shi kad’ai yake zuba murmushi a duk sanda ya tuna daren Alfaharinsa.
Karfe hud’u na yamma ya had’o yanasa yanasa yadawo gida don ya kasa aikin kirki.
Ku biyo mu
SAFHA….
0 Response to "INA DA BURI kashi na 9"
Post a Comment