INA DA BURI kashi na 17

*INA DA BURI*
MARYAM ADAM
FEENAT JA’AFAR
             &
HAFSAT ISMAIL (MMN HANEEF)
17_Jiki ya zare a hankali jin ana kiran sallah sai kwa warai! Ta bud’e ido tare da sauke shi bisa kanshi ciri da tuhuma.
Yake yai mata,dan haka tuni ta sau kuka tana tatta6e baki kamar na shagwa6a66un yara tana shusshura k’afa wanda ya sanya shi sauka da sauri yana dariyar keta ya shige band’aki ganin ta rarumo pillow.
Lalle kam Deeja ta iya salo na nad’e taburmar kunya,yanzun zata nutsu ta amshi messages daga baya ta hau mishi bori,sai dai yau yasan sai ya toshe kunne dan mita, dan dama shi din mai laifi ne.
****
Soyayya tsantsa Kamal ke zubawa da budurwarshi wacce yake nuna ma Deeja yadda yake sonta tamkar ranshi. 
Ya daina waya da ita a d’aki, koh ta kira koh shi ya kira sai ya fita parlour dan gudun masifar Deeja.
Sam ita ba wayarshi ba ce take bata haushi sama da yadda yaki zuciya ya sallameta.
Kwance yake saman kujera yana waya yana murmushi wanda daka nufo gunshi zaka fahimci tsabar walwala kwance a fuskarshi.
A kanshi ta tsaya rike da k’ugu tana hura hanci.
Ido ya sa mata tare da fad’in
“Bari zan kira ki..
Harara ya sau mata tare da kashe wayar saboda gudun kar ta kwafsa mashi. 
Tashi yai tare da zama yana latsa waya tare da fad’in
“Ya aka yi?
Baki ta ta6e tare da fad’in
“Ina zancen mu ya kwana? Dan kasan Allah? Toh na gaji.
Kai ta d’auke tana jijjiga rike da k’ugu.
Murmushi yai tare da jingina da kujerar yana kallonta.
“Toh ya ki ke so ayi?
A fusace ta ce
“Ka sallame ni kawai..
Ido ya sa mata hannu bisa ha6a.
“Shine matsalar?
Kai ta jijjiga da sauri
“Kwarai kuwa.
“Toh bazan sallama ba,sai mey kuma?
A zabure ta sau kugun tare da fad’in
“Ai kwa yau baka isa ba,dan bazan ta6a zama naga shirmen auren nan naka ba,bayan na tafi ka auro dubu chan ta matse ka bani ba.
Murmushi ya yi tare girgizaKai.
“D’aya ma ta ishe ni rayuwa, amma dole ki zama ‘yar kallo,dan fa bazan saki ba,aure kuma ba fashi.
Daga hakan ya tashi yana latsar waya ya barta gurin tsaye tana huci tamkar namijin zaki.
***
Bayan kwana biyu abubuwa sun k’ara jagulewa tsakanin Kamal da Deeja, kowa ya fita sabgar wani sai dai Deeja na da bak’in cikin abinda Kamal ke yi mata wanda take ganin tsabar mugunta ce.
Da shirinshi ya fito na fita office ta tareshi tana masifar sai fa ya sallameta,dan jiya har tai bacci tana jiyo sautin dariyarshi.
“Kar ki 6atamin rai don Allah, saboda ina so na fita cikin farin ciki da annuri fuska na min walwali dan so nake in fara tozali da sahibata, Ok?…
Baki ta saka tana kallonshi,dan haka sai ya ware mata yatsunshi biyu tare da karkatar da kai ya ce
“Bye-bye..
Daga hakan ya ra6a ta gefenta ya fice daga gidan yana dariyar mugunta.
Wani irin bak’in ciki ne ya k’ara rufeta wanda yasa ta kai zaune bata shirya ba ta sau kuka.
Ba dan tuno da zancen Abba da yau ta tafka rashin mutunci tai gida.
Gidan Maman Ihsan ta shiga,ita kad’ai take ganin zata iya fad’i ma kukanta, duk da koh shawarar ta bata ba lalle ta dauka ba.
Ajiyar zuciya Maman Ihsan din tayi bayan ta gama saurarenta.
“Wannan ranar nake guje miki a kullum Deeja,sai dai ke abinda ke gaba gareki kawai ki ke yi,yanzu ne zaki rintse ido,dan fa zaki ga abu iri-iri.
Baki ta ta6e 
“Ni fa ba kishi nake ba,burina kawai ya sallameni.
Ido ta sa mata,ta ma rasa mey zata fad’a mata,dan haka ido kawai ta sa mata karshe dai da fad’a suka rabu.
Yinin ranar ko abinda zata ci bata tashi ta nema ba har Kamal ya dawo daga gurin aiki tana kunci.
Da sallama ya shigo yana yar waka,dan haka da harara ta bishi,daga shi har sallamar ta watsar su gefe.
D’aki ya shiga ya rage kayan jikinshi sannan ya fad’a kitchen saboda ganin gurin cin abinci wayam alamar bata girka ba yau.
Girkinshi yake yi hankali kwance yana waya had’e da murmushi cikin aminci rike da serving spoon.
Kwafa tayi tare da kunna tv amma har lokacin tana tsintar firarshi hankali kwance cikin ‘husky voice’.
“Kinga ai dole na shiga kitchen na girka tunda bani da mai yi min, sai dai nasan cewa daga ranar da kika shigo gidan nan ko spoon ba zan k’ara rik’ewa ba ballantana shiga kitchen girki”…
Dariya ya danyi tare da fad’in
“Of course dorling.
Dariya ya kyalkyale da ita,dan haka da sauri ta makawa kitchen din harara.
Tashi tai tare da isa kitchen d’in ta bud’e fridge ya dan juyo like da waya a kunne.
Harara ta sau mishi tare da tsiyaya ruwa a cup,dan haka sai ya juya tare da kok’arin juya abincin shi yana fad’in
“You know, when we’re together I can truly be myself, and that makes all the difference….
Kinsan dalili?
Ruwan take kur6a tare da kasa kunne tana kwankwada.
Jim yai tare da yin y’ar dariya halamun saurare tare da fad’in “Eh man,cos you’re are the girl of my dream,and I love yo..
Ruwan ta sauke tare da fara tari halamun ta kware jin wannan kalmomi.
Wayar ya cire a kunne tare da juyo wa yana kallonta, baki ta chunno tare da rufe fridge din da dan karfi taja tsaki ta fuce.
Wayarshi ya cigaba da yi ya batta da sintiri daga d’aki zuwa parlour.
Hakan ya gama ya tu6e ya shiga wanka, inda hankalin Deeja ya gaza kwanciya,yau dole ta takawa shegiyar nan birki domin taji ita ta kira,dan haka ta tashi ta d’auki wayar tare da duba last call nashi ta duba.
Cikin sauri ta d’auko wayarta tana kwashe lambar tana sakawa a tata wayar da niyyar kiran kowace ta ci mata zarafi,su kare a waje amma banda cikin gidanta.
Tana saka lambar tana ganin sunan Muneerat na appearing, idonta ta fara murzawa sannan ta k’ara duba lambar tana k’ara sakawa, again Muneerat ta gani. 
Wani irin uban ihu ta kurma wanda ya fitar da Kamal daga toilet d’aure da towel a k’ugunshi yana fad’in
“Lafiya?
SAFHA…✍🏻


SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "INA DA BURI kashi na 17"

Post a Comment