INA DA BURI kash na 13
*INA DA BURI 13*
MARYAM ADAM.
FEENAT JA’AFAR
&
HAFSA(MAMAN HANIF).
13_A zube take bisa kan tiles tayi d’ai d’aya cikin kukanta tamkar an aiko mata Mamy ta mutu,sai kunji kuka take.
13_A zube take bisa kan tiles tayi d’ai d’aya cikin kukanta tamkar an aiko mata Mamy ta mutu,sai kunji kuka take.
Cike da sand’a ya turo
kofar yana mai cije hak’ora kamar mai tsoron kar taji.
Galala ya yai ganin yana yin da take ciki,tuni ya fara kunshe dariya ta juyo.
Galala ya yai ganin yana yin da take ciki,tuni ya fara kunshe dariya ta juyo.
Kukan ta bari tare da
zuba mishi ido,kan yai magana har ta zabura tai yo kanshi da gudu ta
ruk’unk’umo shi tana kuka.
Dariyar ya bari tare
da sauya fuska cike da mamaki,tunaninshi shin mey hakan yake nufi?
Ba dai Deeja ta damu da rashin dawowarshi bane?
Ba dai Deeja ta damu da rashin dawowarshi bane?
Dago kanta yai idonta
rintse tana shesshekar kuka da fad’in
“Wallahi na zata wani
abu ne ya faru,tunani na koh ka mutu ne…
Rai yai saurin had’e
wa jin zancenta tare da maka mata harara.
“Muguwa kawai,in na
mutu ai nasan bakki asara.
Ran itama ta had’e tare da kwace jikinta ta hau nad’e taburmar kunya.
Ran itama ta had’e tare da kwace jikinta ta hau nad’e taburmar kunya.
“Da wa ya damu da ka
mutu koh kai rai? Ka san dai ba damuwata bace,dan tabbas bani da asara.
Kai ya jijjiga tare da
ajiye flaks din d’an waken,yasan koh ba komai ai taji jiki.
Wuce wa yai hanyar d’aki yana kunshe dariya,kan ya zata tasha gabanshi.
Wuce wa yai hanyar d’aki yana kunshe dariya,kan ya zata tasha gabanshi.
“Sai ka fad’a min inda
ka kwana?
Rai ya had’e tare da
dubenta.
“Ina ki ka aike ni?
K’ugu ta rike tare da
fad’in
“Kana nufin tun jiya
d’an wake ka ke nema?
Kai ya jijjiga da sauri tare da fad’in
Kai ya jijjiga da sauri tare da fad’in
“Shine amsar,dan cike
na samu layi a gidan,kinga dole nabi sahu sai yau yazo kaina…
Kallon kar ka rainan
wayo tai mishi.
“Gidan wace matar ne
za’a je a samu d’an wake a wannan daren balle har a samu layi har yau?..
Kai ya ka’rkar da sauri tare da fad’in
Kai ya ka’rkar da sauri tare da fad’in
“Oooo,ashe kin san ba
a inda zan samo d’an wake cikin tsohon daren amma ki ka fidda ni?
Baki ta chunno tare da
d’auke kai jin ta kwafsa.
Kai ya jijjiga tare da
fad’in
“Good,dan kiyi wa
kanki..
D’aki ya shiga ya batta sai masifa take na fad’in toh mey ya cinyeta? Mugu ai dama yasan mey ya had’a, kuma baza’a ci dan waken ba.
D’aki ya shiga ya batta sai masifa take na fad’in toh mey ya cinyeta? Mugu ai dama yasan mey ya had’a, kuma baza’a ci dan waken ba.
Kofa ya turo yana daga
mata kafad’a, yasan yai mata d’aya, ba ta inda zata huce takaici,dan haka
dariya ya rika dirka kan daga bisani ya bi lafiyar gado dan yasha shayi gun
Hadi.
Bayan yaci abinci rana yai wanka ya fuce dan har lokacin da harara kawai take binshi da kwafa,yasan ba yadda zatai dashi sai hak’uri.
Maman Ihsan ce ta shigo jin ya fita da mota.
Bayan yaci abinci rana yai wanka ya fuce dan har lokacin da harara kawai take binshi da kwafa,yasan ba yadda zatai dashi sai hak’uri.
Maman Ihsan ce ta shigo jin ya fita da mota.
Cike da tuhuma take
kallonta dan har kukanta na duben Kamal tana jiyo wa a tsakar gida.
Koh da ta tambayi
ba’asi ba abinda ta 6oye mata.
Kai ta jijjiga,
Kai ta jijjiga,
“Mugun dad’i ne yai
miki yawa,amma ki sani kina wasa ne da damarki,zan so kiyi amfani da ita tun
kamin ta ku6uce miki,dan miji ba abokin hamayya bane,gashi a karshe ke ya bari
da kukan da na sani..
Da sauri ta girgiza
mata kai halamun a’a ne.
“Ni ba shi nake wa kuka ba,tsoron duk girman gidan nan yadda ni kad’ai aciki ne kawai ya sani kuka,amma dan tani ya mutu ma man shi ta shafa bani ba…
“Ni ba shi nake wa kuka ba,tsoron duk girman gidan nan yadda ni kad’ai aciki ne kawai ya sani kuka,amma dan tani ya mutu ma man shi ta shafa bani ba…
Murmushi Maman Ihsan
din tayi tare da jijjiga kai,bata jin ta ta6a cin karo da mai shegen taurin kan
Deeja,amma ta sani Kamal ne kad’ai maganinta,abu d’aya take guje mata yadda
take wasa da damarta, dan in auren soyayya ne taga kawarta da mijinta, dan
soyayya a titi har ‘love birds’ ace ce musu.
Kai ta jijjiga.
Kai ta jijjiga.
A rayuwa ta sani Deeja
abinda ke gaba gareta kawai take duba,amma Insha-Allah wataran zata kai ta
gidan k’awarta,tasan daga ranar Deeja sai ta sauke Buri da rayuwar soyayya
zallah a gidan Miji..
Murmushi tai mata,dan a zahiri koh ita bata yarda cewar Deeja na da ciki ba,dan a d’an zamansu ta fara karantar halinta da tsabar kafiyar ta.
Murmushi tai mata,dan a zahiri koh ita bata yarda cewar Deeja na da ciki ba,dan a d’an zamansu ta fara karantar halinta da tsabar kafiyar ta.
Zancen tace a bari,dan
wai koh sunan Kamal taji yana sa ta kara jin haushin shi.
Sallama tai mata lokacin karfe biyar da wani abu ganin Kamal din ya shigo.
Sallama tai mata lokacin karfe biyar da wani abu ganin Kamal din ya shigo.
Koma wa yai bayan ya
d’akko mata hijab tare da fad’in da bako suke, sai murmushi yake yana jijjiga
kai,da kallo ta bishi,tabbas da abinda yake neman had’a mata.
Nurse ne rike da yar akwati dasu abin auna ‘Bp’.
Nurse ne rike da yar akwati dasu abin auna ‘Bp’.
“Bissmillah karaso
ciki.
Tsaye ta mike tare da
fara raba ido had’i da tattaro yawun bakinta ji ka ke kwat! Ta had’iye.
Kallota ya yi,a duniya
yasan ba abinda ta tsana sama da allura,yasan ta hakan ne kawai zai gane
gaskiyar lamari.
“Sannu madam..
“Sannu madam..
Ido a ware take kallon
Kamal din gabanta na fad’uwa ta kasa koh amsa sannun Nurse.
“Gata nan dai Ishak,ka
ganta nan tun samun cikinta laulayi ta kasa sukuni,yau zazzabi gobe ciwan
kai,gashi in ta fara k’ak’arin amai har tausayinta nake ji…
Wani yawun ta sake had’iye wa tana goge zufa tare da sake waro ido.
Wani yawun ta sake had’iye wa tana goge zufa tare da sake waro ido.
Lalle ne in baka iya
kama barawo ba shi sai ya kamo ka..
Tsayuwa ta gyara ganin
yana fito da ruwa na karin ruwa da allurai,da sauri ta fara in ina.
“Malam ni fa lafiya ta kalau wallahi, ba wani zazzabin da nake da amai..
“Malam ni fa lafiya ta kalau wallahi, ba wani zazzabin da nake da amai..
Da sauri Kamal din ya
amshe da fad’in
“Rabu da ita Ishak
haka take in taga allura,amma mace mai lalurar ciki ai sai da protection,har da
ta tetanus ma kai mata..
Lalle kam Kamal ya wuce tunaninta,dan haka gaba dole ta iya bakinta da tukunta,gashi yanzu yai mata back to sender,dan haka da azama ta karyata kanta da kanta.
Lalle kam Kamal ya wuce tunaninta,dan haka gaba dole ta iya bakinta da tukunta,gashi yanzu yai mata back to sender,dan haka da azama ta karyata kanta da kanta.
“Wallahi ni k’arya
nake,ni bani da wani ciki,dan haka ba allurar da za’a min da raina da kuma
lafiyata..tab,humm.
Kai ta juyar tare da matsawa gefe tana aiko mishi da harara,shi kam bai mamaki ba,dama bai sa a ka ba,amma dan ya taka mata birki yake son sanin gaskiyar lamari,gashi tun kan ai nisa ta karyata kanta,dan haka da sauri ya ce
Kai ta juyar tare da matsawa gefe tana aiko mishi da harara,shi kam bai mamaki ba,dama bai sa a ka ba,amma dan ya taka mata birki yake son sanin gaskiyar lamari,gashi tun kan ai nisa ta karyata kanta,dan haka da sauri ya ce
“Karya take,dan haka
baki isa a fita daga gidan nan ba tare da an juna miki ruwa da allurai ba,dan
kin san na sani da kullum sai kinyi amai kusan sau goma,koh so ki ke ki yanke
jiki ki fad’i ruwan jikin ki ya kare?..
Murmushi Nurse din yai tare da kad’a kai,ya sani da mata akwai tsoron allura,dan haka sai ya ce
Murmushi Nurse din yai tare da kad’a kai,ya sani da mata akwai tsoron allura,dan haka sai ya ce
“Kiyi hak’uri madam
ayi a nutse mu gama,guda uku ce kawai sai ruwa hud’u..
Ido ta zaro tare da bud’e baki,kamin ya sake magana har ta sau kuka,fad’i take ita sam karya take,lafiyarta lau dan haka ba mai kasheta da ranta.
Ido ta zaro tare da bud’e baki,kamin ya sake magana har ta sau kuka,fad’i take ita sam karya take,lafiyarta lau dan haka ba mai kasheta da ranta.
Kanta Kamal din ya
nufa batai tsammani ba ya chafko hannunta,
“Ai kinyi kad’an, naki
wasa ne,dan fa ba kuka ba koh suma ki ke sai an miki..
“Wayyo Mamy na shiga uku.. Wallahi karya nake maka ka rufa min asiri Kamal,bazan sake ba kaji na rantse..
“Wayyo Mamy na shiga uku.. Wallahi karya nake maka ka rufa min asiri Kamal,bazan sake ba kaji na rantse..
Kai ya girgiza mata
yana mai kunshe dariyarshi dan kar ta gane,a take yai rantsuwa da sai fa an
mata,zo ka ga Deeja gwiwa bibbiyu gaban Kamal tana rokon yai mata rai ganin
Nurse na zoko ruwan allura.
SAFHA..
0 Response to "INA DA BURI kash na 13"
Post a Comment