INA DA BURI kash na 13

*INA DA BURI 13*
MARYAM ADAM.
FEENAT JA’AFAR
         &
HAFSA(MAMAN HANIF).
     13_A zube take bisa kan tiles tayi d’ai d’aya cikin kukanta tamkar an aiko mata Mamy ta mutu,sai kunji kuka take.
Cike da sand’a ya turo kofar yana mai cije hak’ora kamar mai tsoron kar taji.
Galala ya yai ganin yana yin da take ciki,tuni ya fara kunshe dariya ta juyo.
Kukan ta bari tare da zuba mishi ido,kan yai magana har ta zabura tai yo kanshi da gudu ta ruk’unk’umo shi tana kuka.
Dariyar ya bari tare da sauya fuska cike da mamaki,tunaninshi shin mey hakan yake nufi?
Ba dai Deeja ta damu da rashin dawowarshi bane?
Dago kanta yai idonta rintse tana shesshekar kuka da fad’in
“Wallahi na zata wani abu ne ya faru,tunani na koh ka mutu ne…
Rai yai saurin had’e wa jin zancenta tare da maka mata harara.
“Muguwa kawai,in na mutu ai nasan bakki asara.
Ran itama ta had’e tare da kwace jikinta ta hau nad’e taburmar kunya.
“Da wa ya damu da ka mutu koh kai rai? Ka san dai ba damuwata bace,dan tabbas bani da asara.
Kai ya jijjiga tare da ajiye flaks din d’an waken,yasan koh ba komai ai taji jiki.
Wuce wa yai hanyar d’aki yana kunshe dariya,kan ya zata tasha gabanshi.
“Sai ka fad’a min inda ka kwana?
Rai ya had’e tare da dubenta.
“Ina ki ka aike ni?
K’ugu ta rike tare da fad’in
“Kana nufin tun jiya d’an wake ka ke nema?
Kai ya jijjiga da sauri tare da fad’in
“Shine amsar,dan cike na samu layi a gidan,kinga dole nabi sahu sai yau yazo kaina…
Kallon kar ka rainan wayo tai mishi.
“Gidan wace matar ne za’a je a samu d’an wake a wannan daren balle har a samu layi har yau?..
Kai ya ka’rkar da sauri tare da fad’in
“Oooo,ashe kin san ba a inda zan samo d’an wake cikin tsohon daren amma ki ka fidda ni?
Baki ta chunno tare da d’auke kai jin ta kwafsa.
Kai ya jijjiga tare da fad’in
“Good,dan kiyi wa kanki..
D’aki ya shiga ya batta sai masifa take na fad’in toh mey ya cinyeta? Mugu ai dama yasan mey ya had’a, kuma baza’a ci dan waken ba.
Kofa ya turo yana daga mata kafad’a, yasan yai mata d’aya, ba ta inda zata huce takaici,dan haka dariya ya rika dirka kan daga bisani ya bi lafiyar gado dan yasha shayi gun Hadi.
Bayan yaci abinci rana yai wanka ya fuce dan har lokacin da harara kawai take binshi da kwafa,yasan ba yadda zatai dashi sai hak’uri.
Maman Ihsan ce ta shigo jin ya fita da mota.
Cike da tuhuma take kallonta dan har kukanta na duben Kamal tana jiyo wa a tsakar gida.
Koh da ta tambayi ba’asi ba abinda ta 6oye mata.
Kai ta jijjiga,
“Mugun dad’i ne yai miki yawa,amma ki sani kina wasa ne da damarki,zan so kiyi amfani da ita tun kamin ta ku6uce miki,dan miji ba abokin hamayya bane,gashi a karshe ke ya bari da kukan da na sani..
Da sauri ta girgiza mata kai halamun a’a ne.
“Ni ba shi nake wa kuka ba,tsoron duk girman gidan nan yadda ni kad’ai aciki ne kawai ya sani kuka,amma dan tani ya mutu ma man shi ta shafa bani ba…
Murmushi Maman Ihsan din tayi tare da jijjiga kai,bata jin ta ta6a cin karo da mai shegen taurin kan Deeja,amma ta sani Kamal ne kad’ai maganinta,abu d’aya take guje mata yadda take wasa da damarta, dan in auren soyayya ne taga kawarta da mijinta, dan soyayya a titi har ‘love birds’ ace ce musu.
Kai ta jijjiga.
A rayuwa ta sani Deeja abinda ke gaba gareta kawai take duba,amma Insha-Allah wataran zata kai ta gidan k’awarta,tasan daga ranar Deeja sai ta sauke Buri da rayuwar soyayya zallah a gidan Miji..
Murmushi tai mata,dan a zahiri koh ita bata yarda cewar Deeja na da ciki ba,dan a d’an zamansu ta fara karantar halinta da tsabar kafiyar ta. 
Zancen tace a bari,dan wai koh sunan Kamal taji yana sa ta kara jin haushin shi.
Sallama tai mata lokacin karfe biyar da wani abu ganin Kamal din ya shigo.
Koma wa yai bayan ya d’akko mata hijab tare da fad’in da bako suke, sai murmushi yake yana jijjiga kai,da kallo ta bishi,tabbas da abinda yake neman had’a mata.
Nurse ne rike da yar akwati dasu abin auna ‘Bp’.
“Bissmillah karaso ciki.
Tsaye ta mike tare da fara raba ido had’i da tattaro yawun bakinta ji ka ke kwat! Ta had’iye. 
Kallota ya yi,a duniya yasan ba abinda ta tsana sama da allura,yasan ta hakan ne kawai zai gane gaskiyar lamari.
“Sannu madam..
Ido a ware take kallon Kamal din gabanta na fad’uwa ta kasa koh amsa sannun Nurse.
“Gata nan dai Ishak,ka ganta nan tun samun cikinta laulayi ta kasa sukuni,yau zazzabi gobe ciwan kai,gashi in ta fara k’ak’arin amai har tausayinta nake ji…
Wani yawun ta sake had’iye wa tana goge zufa tare da sake waro ido.
Lalle ne in baka iya kama barawo ba shi sai ya kamo ka..
Tsayuwa ta gyara ganin yana fito da ruwa na karin ruwa da allurai,da sauri ta fara in ina.
“Malam ni fa lafiya ta kalau wallahi, ba wani zazzabin da nake da amai..
Da sauri Kamal din ya amshe da fad’in
“Rabu da ita Ishak haka take in taga allura,amma mace mai lalurar ciki ai sai da protection,har da ta tetanus ma kai mata..
Lalle kam Kamal ya wuce tunaninta,dan haka gaba dole ta iya bakinta da tukunta,gashi yanzu yai mata back to sender,dan haka da azama ta karyata kanta da kanta.
“Wallahi ni k’arya nake,ni bani da wani ciki,dan haka ba allurar da za’a min da raina da kuma lafiyata..tab,humm.
Kai ta juyar tare da matsawa gefe tana aiko mishi da harara,shi kam bai mamaki ba,dama bai sa a ka ba,amma dan ya taka mata birki yake son sanin gaskiyar lamari,gashi tun kan ai nisa ta karyata kanta,dan haka da sauri ya ce
“Karya take,dan haka baki isa a fita daga gidan nan ba tare da an juna miki ruwa da allurai ba,dan kin san na sani da kullum sai kinyi amai kusan sau goma,koh so ki ke ki yanke jiki ki fad’i ruwan jikin ki ya kare?..
Murmushi Nurse din yai tare da kad’a kai,ya sani da mata akwai tsoron allura,dan haka sai ya ce
“Kiyi hak’uri madam ayi a nutse mu gama,guda uku ce kawai sai ruwa hud’u..
Ido ta zaro tare da bud’e baki,kamin ya sake magana har ta sau kuka,fad’i take ita sam karya take,lafiyarta lau dan haka ba mai kasheta da ranta.
Kanta Kamal din ya nufa batai tsammani ba ya chafko hannunta,
“Ai kinyi kad’an, naki wasa ne,dan fa ba kuka ba koh suma ki ke sai an miki..
“Wayyo Mamy na shiga uku.. Wallahi karya nake maka ka rufa min asiri Kamal,bazan sake ba kaji na rantse..
Kai ya girgiza mata yana mai kunshe dariyarshi dan kar ta gane,a take yai rantsuwa da sai fa an mata,zo ka ga Deeja gwiwa bibbiyu gaban Kamal tana rokon yai mata rai ganin Nurse na zoko ruwan allura.
SAFHA..


SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "INA DA BURI kash na 13"

Post a Comment