CANJIN YANAYI 6
©MARYAM ADAM
“Wannan
ɓangaren wani lokaci wasu iyaye ke cutar yaransu da kansu wallahi, saboda uwa
itace makarantar yaranta, abinda suka ga kina yi shi zasu ɗauka, ko kuma ki
koyar dasu duk daren Allah suyi wanka kamin su kwanta bacci, in har suka saba
da hakan to zaki ga ko basa yi a koyaushe zakiga sunyi saboda CANJIN YANAYI na
zafi domin suji daɗin kwanciya su kansu, amma ke uwa kinzo kin dunk’ula kin
kwanta da k’arnin hayak’i ga zufa me zai hana yaranki bazasu ɗauki ak’idarki
ba”.
“Wata uwa ma yaran na son suyi wankan zata rik’a hanasu da cewa wallahi ku raba kanku da muguwar murar zafin nan bata wasa da kama mutum, daga hakan sai kiga yaro ya ɗauka ya zauna akai”.
“Tabbas hakane”, faɗar Zainab, kana ta ɗora da cewa’ “kinganni nan Anty na tayi silar hakan a gareni, saboda iyayenmu sun rasu tun muna yara a hannunta na tashi, wallahi bata wanka hakan take kwanciyarta ina gidan yayi aure suka dinga gwabzawa da kishiyar har Mijin ya ɗauke amaryar yaje garin da yake aiki da ita, ko wannan kishin da kike gani itace ke k’ara zugani akai wai in nayi sake dai naga yanda aka yi mata”.
“Ai ko dukanku kunyi sake wallahi, don hanyarda kuka hau ba mai ɓullewa bace, sai dai sauk’in abin ke kina da sauran dama ta gyara kuskurenda kika tafka don haka ki kula ki natsu kigane tsabta itace mataki na farko a zamantakewa ta aure, in har baki da tsabta wallahi duk wani felek’enki na banza ne, kuma za’a yi babu ke”.
“Yanzu abinda nake so ki rik’e shine ki kula da wankan jikinki ak’alla sau uku a wuni musamman lokacin zafi, kuma kowanne wankan ki haɗa shi da brush ke kanki zakiji sauyi ba mijin ba kaɗai”.
Hakan dai ta yita ɗorata a hanya har ta fahimci komai wanda yasa take k’ara jin Bebeelo har cikin ranta, da hakan ta rakata ta wuce gida wurin k’arfe 9:00pm.
*****
Samui-samui ta shiga gidan tana sanɗa har ta faɗa ɗakinta, wanda bata son kowa ya ganta daga Mijin har kishiyar tata, sai yanzu take nadamar felek’enda tayi ta yiwa Maman Farha da iyayi, ashe duk na banza ne don ta fita matsayi gun Mijin, abinda yakamata ace tayi ta kula dashi ba shine gabanta ba sai ɗan banzan kishi da Anty Aisha take aon ɗorata akai.
A yanzu ne ya kamata ta fahimci biyu babu ne Antyn takeson ayi, yanda ta kasa gane gidan aurenta itama ta ɓata mata nata, don haka yanzu ta k’uɗurtama ranta zama da Maman Farha da zuciya ɗaya ita da yaranta, sai kuma uwa uba Maigidan da kanshi da zata zage damtse wurin kula da kanta kyautatawa da sauransu.
****
Washe gari da yamma ta gama girkinta taje ta tsala wanka da kwalliya taji ta gani sai k’amshi take zabgawa. Falon nashi tayi zaune tana jiran shigowarshi, bayan ya shigo ne ta tashi ta taryoshi da murnarta da fara’a kwance a fuskarta, sai dai kan datake nok’ewa alamar jin kunya.
Kallon mamaki yaa bita dashi inda ta tayashi cire kayan jikinshi yana biye da ita tamkar rak’umi da akala har ya shiga bayi wanka, tunani ne fal ranshi har yayi wankan ya fito ya saka jallabiyarshi.
Fita tayi ɗakin Maman Farha ta kirata, sannan ta rungumo Azeema saman kafaɗarta tana yi mata wasa har suka zo falon, ita ta sakawa kowa abinci sannan ta ɗora Azeema saman cinyarta in taci cokali ɗaya ta saka mata itama a baki.
Ta wutsiyar ido ya dinga kallon Hafsat yaga wane yanayi take ciki, inda suka haɗa ido kowannensu yayi murmushi mai nuna alamar jin daɗin CANJIN YANAYIN da aka samu sannan suka ɗauke kansu, saboda yau ba wani felek’e ko iyayi daga Zainab, kowannensu yana mamakin hakan har suka k’are cin abincin inda Azeema tayi bacci saman jikinta.
Hafsat ce ta mik’o hannu zata karɓeta Zainab ta mik’e tace’ “muje ɗakin na shimfiɗe maki ita”. Hakan ta wuce Hafsat ta bita a baya tana rik’e da hannun su Farha suka wuce ɗakin nata.
Sai 11:00pm taga ya gama ayukkanshi na office ya yi shirin bacci, hakan yasa yana shiga wanka itama taje ɗakinta ta darje jikinta da kyau. Wurin brush ne ni kaina na dinga yi mata dariya, saboda inaga ta saka makilin yafi sau uku tana wanke bakin sannan ta kammala ta fito ta kimtsa ta wuce ɗakinshi.
Yau waje yace suyi shimfiɗa saɓanin kullum da suke shigewa uwar ɗaka a kunna A.C, bayan sun kwanta ne ta shige cikin jikinshi ne ta kira sunanshi yana amsawa ta fara da cewa’
“Yanzu Kabeer a tunaninka wannan abin da kayimin haka zamantakewa tace?, a tunanina kaine mutum na farko da zai fara hango kuskurena yace min Zainab abu kaza da kikayi bai dace ba ki gyara kiyi kaza kiyi kaza, amma ka zubamin ido inata felek’e akai ashe aikin banzane ga inda ya kamata nayi gyara nan domin shine tubalin zama”.
“Kiyi hak’uri Zainab a kullum inaso nayi maki magana sai inga abin tamkar cin fuskane ko cin zarafi, shiyasa nayita aikata wasu abubuwan ko zaki fahimci CANJIN YANAYI ki gyar amma kuma sai abin ya faskara, amma wallahi ina gab da zaunarda ke mu fahimci juna in gaya maki abinda ke raina, sai gashi kin hango kin gyara da kanki, kuma gaskiya naji daɗin kasancewar hakan”.
“Aka dai lurar dani”.
“Bangane aka dai lurar da ke ba”.
“Eh to tunda kai da hakkin yake saman kanka ka kasa to ansamu wacce ta lular dani kuma naji daɗi da hakan sosai wallahi”.
Lallashinta ya dingayi sannan ta gaya mai yanda sukayi da Bebeelo bata ɓoye mashi komai ba, ba k’aramin daɗi yaji ba har yana halayyar wannan matar saboda ba k’aramar lada ta samu ba da yin hakan, nan dai suka tattauna ya k’ara bata hak’uri kan laifinshi data gani na rashin gaya mata kuskurenta. Ni dai Jegal can na hango bakinsu a haɗe nayi saurin fitowa na ja masu k’ofa saboda kar su cinye halshen juna a gaban idona, _lolx_ Asuba tagari.
****
Washe gari ma hakan suka ga CANJIN YANAYI sosai, don kayan baccin da har ta haɗa kalaci suna saye a jikinta yau babu su sai dai wankan da tayi ta saka kayanta marar nauyi suka zauna kalaci kowa na zabga k’amshi.
****
Bayan ya fito wanka ne ya matsawa Hafsat kan cewa ta shiga bayinshi tayi wanka inda itako tayi tsaye kan cewa ba zata shiga ba har sai ya gaya mata me yagama ɓoyo a bayin tukuna.
Zaunar da ita yayi yana gaya mata CANJIN YANAYIN da ya samu daga Zainab, ya ɗora da cewa’ “ba da wata manufa na hanaki wanka a bayina ba, nayi hakan ne ko Zainab zata fahimci cewa sai kinyi wanka kike shigowa ɗakina itama ta dinga yin hakan”.
“Shimfiɗa da kike mana a waje ranar girkinta kuma mu kwana ɗaki shine….”.
Saurin tarar numfashinshi tayi da cewa’ “wannan sirrinka ne tsakaninka da matarka bai dace ka gayamin ba, yanzu dai na fahimci dalilinka na hanamin shiga bayinka”.
Tsam ta tashi ta faɗa bayin domin yin wanka. Tunani yake aranshi da za’a samu mata masu halayyar Hafsat da zama ya wuce inda ake tsammaninshi, shi dai har gurin ubangiji ba ɗabi’arshi bace ta kaiwa ɗaya maganar ɗaya ba, ko yanzu yayi hakan ne saboda fita zargin Hafsat na yana hanata wanka bayinshi yana bari Zainab nayi, saboda ko kwanciyarsu ɗaki da Zainab dole ce saboda sanyin A.C zai rage mashi jin bashin jikinta ne.
Tun daga wannan lokacin zaman lafiya ya ɗore tsakanin Zainab da Hafsat, ba wai basa kishin junansu bane a’ah sunayi sai dai cikin hikima da hankali tunda Zainab ta fahimci CANJIN YANAYI tsakanin zafi da sanyi da damana na kula da jikinta.
TAMMAT BI HAMDILLAH
Anan na kawo k’arshen wannan gajeren labari nawa, kuskurenda ke ciki Allah ya yafemin, ku kuma ya baku ikon ɗaukar darasin da ke ciki.
MASOYANA
Na gaisheku a duk inda kuke, ina k’aunarku! Ina k’aunarku!! Ina k’aunarku!!!.
“Wata uwa ma yaran na son suyi wankan zata rik’a hanasu da cewa wallahi ku raba kanku da muguwar murar zafin nan bata wasa da kama mutum, daga hakan sai kiga yaro ya ɗauka ya zauna akai”.
“Tabbas hakane”, faɗar Zainab, kana ta ɗora da cewa’ “kinganni nan Anty na tayi silar hakan a gareni, saboda iyayenmu sun rasu tun muna yara a hannunta na tashi, wallahi bata wanka hakan take kwanciyarta ina gidan yayi aure suka dinga gwabzawa da kishiyar har Mijin ya ɗauke amaryar yaje garin da yake aiki da ita, ko wannan kishin da kike gani itace ke k’ara zugani akai wai in nayi sake dai naga yanda aka yi mata”.
“Ai ko dukanku kunyi sake wallahi, don hanyarda kuka hau ba mai ɓullewa bace, sai dai sauk’in abin ke kina da sauran dama ta gyara kuskurenda kika tafka don haka ki kula ki natsu kigane tsabta itace mataki na farko a zamantakewa ta aure, in har baki da tsabta wallahi duk wani felek’enki na banza ne, kuma za’a yi babu ke”.
“Yanzu abinda nake so ki rik’e shine ki kula da wankan jikinki ak’alla sau uku a wuni musamman lokacin zafi, kuma kowanne wankan ki haɗa shi da brush ke kanki zakiji sauyi ba mijin ba kaɗai”.
Hakan dai ta yita ɗorata a hanya har ta fahimci komai wanda yasa take k’ara jin Bebeelo har cikin ranta, da hakan ta rakata ta wuce gida wurin k’arfe 9:00pm.
*****
Samui-samui ta shiga gidan tana sanɗa har ta faɗa ɗakinta, wanda bata son kowa ya ganta daga Mijin har kishiyar tata, sai yanzu take nadamar felek’enda tayi ta yiwa Maman Farha da iyayi, ashe duk na banza ne don ta fita matsayi gun Mijin, abinda yakamata ace tayi ta kula dashi ba shine gabanta ba sai ɗan banzan kishi da Anty Aisha take aon ɗorata akai.
A yanzu ne ya kamata ta fahimci biyu babu ne Antyn takeson ayi, yanda ta kasa gane gidan aurenta itama ta ɓata mata nata, don haka yanzu ta k’uɗurtama ranta zama da Maman Farha da zuciya ɗaya ita da yaranta, sai kuma uwa uba Maigidan da kanshi da zata zage damtse wurin kula da kanta kyautatawa da sauransu.
****
Washe gari da yamma ta gama girkinta taje ta tsala wanka da kwalliya taji ta gani sai k’amshi take zabgawa. Falon nashi tayi zaune tana jiran shigowarshi, bayan ya shigo ne ta tashi ta taryoshi da murnarta da fara’a kwance a fuskarta, sai dai kan datake nok’ewa alamar jin kunya.
Kallon mamaki yaa bita dashi inda ta tayashi cire kayan jikinshi yana biye da ita tamkar rak’umi da akala har ya shiga bayi wanka, tunani ne fal ranshi har yayi wankan ya fito ya saka jallabiyarshi.
Fita tayi ɗakin Maman Farha ta kirata, sannan ta rungumo Azeema saman kafaɗarta tana yi mata wasa har suka zo falon, ita ta sakawa kowa abinci sannan ta ɗora Azeema saman cinyarta in taci cokali ɗaya ta saka mata itama a baki.
Ta wutsiyar ido ya dinga kallon Hafsat yaga wane yanayi take ciki, inda suka haɗa ido kowannensu yayi murmushi mai nuna alamar jin daɗin CANJIN YANAYIN da aka samu sannan suka ɗauke kansu, saboda yau ba wani felek’e ko iyayi daga Zainab, kowannensu yana mamakin hakan har suka k’are cin abincin inda Azeema tayi bacci saman jikinta.
Hafsat ce ta mik’o hannu zata karɓeta Zainab ta mik’e tace’ “muje ɗakin na shimfiɗe maki ita”. Hakan ta wuce Hafsat ta bita a baya tana rik’e da hannun su Farha suka wuce ɗakin nata.
Sai 11:00pm taga ya gama ayukkanshi na office ya yi shirin bacci, hakan yasa yana shiga wanka itama taje ɗakinta ta darje jikinta da kyau. Wurin brush ne ni kaina na dinga yi mata dariya, saboda inaga ta saka makilin yafi sau uku tana wanke bakin sannan ta kammala ta fito ta kimtsa ta wuce ɗakinshi.
Yau waje yace suyi shimfiɗa saɓanin kullum da suke shigewa uwar ɗaka a kunna A.C, bayan sun kwanta ne ta shige cikin jikinshi ne ta kira sunanshi yana amsawa ta fara da cewa’
“Yanzu Kabeer a tunaninka wannan abin da kayimin haka zamantakewa tace?, a tunanina kaine mutum na farko da zai fara hango kuskurena yace min Zainab abu kaza da kikayi bai dace ba ki gyara kiyi kaza kiyi kaza, amma ka zubamin ido inata felek’e akai ashe aikin banzane ga inda ya kamata nayi gyara nan domin shine tubalin zama”.
“Kiyi hak’uri Zainab a kullum inaso nayi maki magana sai inga abin tamkar cin fuskane ko cin zarafi, shiyasa nayita aikata wasu abubuwan ko zaki fahimci CANJIN YANAYI ki gyar amma kuma sai abin ya faskara, amma wallahi ina gab da zaunarda ke mu fahimci juna in gaya maki abinda ke raina, sai gashi kin hango kin gyara da kanki, kuma gaskiya naji daɗin kasancewar hakan”.
“Aka dai lurar dani”.
“Bangane aka dai lurar da ke ba”.
“Eh to tunda kai da hakkin yake saman kanka ka kasa to ansamu wacce ta lular dani kuma naji daɗi da hakan sosai wallahi”.
Lallashinta ya dingayi sannan ta gaya mai yanda sukayi da Bebeelo bata ɓoye mashi komai ba, ba k’aramin daɗi yaji ba har yana halayyar wannan matar saboda ba k’aramar lada ta samu ba da yin hakan, nan dai suka tattauna ya k’ara bata hak’uri kan laifinshi data gani na rashin gaya mata kuskurenta. Ni dai Jegal can na hango bakinsu a haɗe nayi saurin fitowa na ja masu k’ofa saboda kar su cinye halshen juna a gaban idona, _lolx_ Asuba tagari.
****
Washe gari ma hakan suka ga CANJIN YANAYI sosai, don kayan baccin da har ta haɗa kalaci suna saye a jikinta yau babu su sai dai wankan da tayi ta saka kayanta marar nauyi suka zauna kalaci kowa na zabga k’amshi.
****
Bayan ya fito wanka ne ya matsawa Hafsat kan cewa ta shiga bayinshi tayi wanka inda itako tayi tsaye kan cewa ba zata shiga ba har sai ya gaya mata me yagama ɓoyo a bayin tukuna.
Zaunar da ita yayi yana gaya mata CANJIN YANAYIN da ya samu daga Zainab, ya ɗora da cewa’ “ba da wata manufa na hanaki wanka a bayina ba, nayi hakan ne ko Zainab zata fahimci cewa sai kinyi wanka kike shigowa ɗakina itama ta dinga yin hakan”.
“Shimfiɗa da kike mana a waje ranar girkinta kuma mu kwana ɗaki shine….”.
Saurin tarar numfashinshi tayi da cewa’ “wannan sirrinka ne tsakaninka da matarka bai dace ka gayamin ba, yanzu dai na fahimci dalilinka na hanamin shiga bayinka”.
Tsam ta tashi ta faɗa bayin domin yin wanka. Tunani yake aranshi da za’a samu mata masu halayyar Hafsat da zama ya wuce inda ake tsammaninshi, shi dai har gurin ubangiji ba ɗabi’arshi bace ta kaiwa ɗaya maganar ɗaya ba, ko yanzu yayi hakan ne saboda fita zargin Hafsat na yana hanata wanka bayinshi yana bari Zainab nayi, saboda ko kwanciyarsu ɗaki da Zainab dole ce saboda sanyin A.C zai rage mashi jin bashin jikinta ne.
Tun daga wannan lokacin zaman lafiya ya ɗore tsakanin Zainab da Hafsat, ba wai basa kishin junansu bane a’ah sunayi sai dai cikin hikima da hankali tunda Zainab ta fahimci CANJIN YANAYI tsakanin zafi da sanyi da damana na kula da jikinta.
TAMMAT BI HAMDILLAH
Anan na kawo k’arshen wannan gajeren labari nawa, kuskurenda ke ciki Allah ya yafemin, ku kuma ya baku ikon ɗaukar darasin da ke ciki.
MASOYANA
Na gaisheku a duk inda kuke, ina k’aunarku! Ina k’aunarku!! Ina k’aunarku!!!.
0 Response to "CANJIN YANAYI 6"
Post a Comment