INA DA BURI kashi na 7

*INA DA BURI7*
FEENAT JAFAR
          &
HAFSA ISMA’IL(MMN HANEEP)
7_ Pillow ta fara hullo mishi tare da d’ane gadon ta tsaya,duk huci suke ganin yadda sukai ta tsere tana zille wa.
“Dama kin bar wahalar da kanki,dan kinji na rantse yau saina seta tunaninkin nan..
“Ka fara saita naka,amma ba dai nawa ba..
Tsalle ta doka da niyar sauka a gadon ganin ya kawo mata raruma ta gurd’e,duk da haka da karfin hali tai hanyar kofa tana cije le6e ya cimmata kamar wasu yara.
Tamkar masu tseren gaske haka suke sauke ajiyar zuciya ya gamata da kofar d’akin.
Ido ta tamke kam ganin yana niyar gama fuskar su ta fara tuttureshi.
“Wane irin mugu ne wai kai?
Murmushi ya yi yana kallon bakin tsiwar.
“Ki tsaya ki amsa da hankali..
“Bana so.. Allah tsare ni ka do6an baki.
Yin duniya ta kasa kwatar kanta,dan haka batai wata-wata ba ta gartsa mishi cizo a hannu iya karfinta da ba shiri ya sauta.
Da dingishi ta nufi hanyar band’aki tana mako mishi harara tare da yarfe hannu jin zugin kafarta.
Kai ya jijjiga shima yana yarfe inda ta cije shi, yau kam wallahi yaso koya mata darasi amma taci sa’a ba wai dan bazai iya kamota ba ta karfi.
“Gobe in na ce ki min girki ki kiyi ki ga yadda zamu karke dake..
 Harara ta maka mishi ganin yana bud’e kofar zai fita.
Ajiyar zuciya ta saka tare da dafe kirji.
“Mugu kawai,cizo yai rana.
     
****
Kitchen take tana dafa indomie da zata ci, ta tsinkayo muryar Zainab mak’ociyarta dake shigowa gidan wasu lokutta. Falon ta fita suka gaisa ta kar6i y’arta Ihsan tana mata wasa.
“Ya naji gidan shiru, ko maigidan baya nan ne?”.
Yatsine fuska ta fara yi kana ta bata amsa da cewa’ “ya fita, yo ma ko yana gidan me zai k’ullata min ne daya wuce takura”.
Murmushi Zainab ta yi tana mai mamakin halayya irin ta Khadeeja, saboda d’an shigowarda take yi ta fahimci cewa akwai takun sak’a tsakaninta da Kamal.
“Gaskiya Khadeeja ni ko ina hango wautarki a wani 6angaren”.
Kallo ta bita dashi mai alamar tambaya, cikin halin ko in kula ta furta’ “wauta fa kika ce Maman Ihsan?, kamar yaya?”. Ta furta hakan tana mai wasa da kalabarda ke saman kan Ihsan.
“Wauta mana, saboda in ba wauta ba mai sankacecen Miji kamar Kamal har zai yi mai rik’on sakainar kashi, kar ki manta yanda tsadaddin Maza suke wuya a wannan lokacin”.
Dariya ta kece da ita har da ubar k’wallarta, saboda yanda maganar ta bata dariya, wai sankacecen Miji, “Kamal baya gabana, saboda INADA BURIN da ba lallai ne Kamal ya iya cikamin shi ba”.
Bud’ar bakin Zainab za tayi magana kenan ta tsinkayo muryar Kamal taja bakinta ta tsuke, nan ta kar6i Ihsan daga hannunta had’e da furta’ “ni zan wuce sai wani lokaci in kin samu lek’o gidan namu”.
A k’ofar shigowa ne suka ci karo dashi ta rakota, nan ya ra6e ya basu hanya suka fice shi ko ya k’arasa daga ciki.
K’amshin girkin da ta d’ora ne ya ja hankalinshi ya fad’a kitchen d’in. Ganin k’aramar tukunya akai ya bashi tabbacin ko miye take girkawa ba dashi take girka shi ba, kuma gashi ya kwaso yunwa da zafin rana.
Filet ya d’auko ya juye indomie d’in ya d’auka ya shige d’aki har da murd’a key, sai da ya rage kayan jikinshi sannan ya yi zaune ya fara kai loma.
****
Baki ne ta saki saboda hango y’ar k’aramar tukunyar da ta d’ora ajiye a gefe, wanda ke nuna an juyen abincin. Dakin kawai ta tunkara ta murd’a k’ofa ta jita a rufe, ji ta yi tamkar ta kurma ihu saboda tabbacin Kamal ne ya juye mata indomie ya shige d’aki yana ci.
“Wallahi ka bud’e k’ofar ka bani abincina, in ba zalunci ba haka kawai za ka zo ka tararda na yi girkina ka juye, hala ni baiwarka ce, ko kuma an kawo ni gidan ne domin in yima girki?”. Masifa take yi tana bugun k’ofar tamkar za ta 6allata.
Yanda kasan bebe haka ya koma mata, sai da ya cinye abincin tass sannan ya fad’a toilet ya yo wanka ya fito ya kimtsa cikin k’ananan kaya sannan ya bud’e d’akin ya fice.
****
Wata indomie ce take dafawa ta yi tsaye tana gadin abarta sai cizon yatsa take yi tana huci tamkar wata kasa.
Cikin sand’a ya k’arasa kitchen d’in wanda dama ta jiyo k’amshin turarenshi, tana batun juyawa ta balbaleshi da masifa taji ya sagalo hannunwanshi duka biyun ya rik’e k’ugunta had’e da kwantar da kanshi saman kafad’arta.
“Yanzu don kin girkawa mijinki abinci ya ci shine abin masifa, ya kamata fa yarinya ki bada kai bori ya hau, saboda nasan kinyi kewar wannan”.
Yana gama fad’a ya juyo da kanta saitin fuskarshi. Baki ta bud’e da niyyar masifa karaf ya had’e bakinsu guri d’aya yana juya halshenshi cikin bakinta, jin cewa jikinta ya saki gaba d’aya ya sake ta had’e da ja baya, sai gashi ta fad’o mai saman jiki.
“Haba Yarinya, karki cemin d’an wannan abin yasa kin kasa d’aukar kanki, wannan ai shafar mai ne”.
Cikin borin kunya ta fizge jikinta daga gareshi ta yi mai wani mugun kallo, sannan ta juye abincinta ta bankad’eshi ta fice inda ya bita da dariyar k’eta.
Muje zuwa
Daga Alk’alamin (SAFHA)…

SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "INA DA BURI kashi na 7"

Post a Comment