CANJIN YANAYI 5


DAGA ALK’ALAMIN Y’AR MUTAN JEGA
©MARYAM ADAM
         Haka kawai yau taji tana son shiga gidan mak’ociyarta kuma k’awarta Bahijja (Bebeelo) nan ta figi gyalenta ta faɗa gidan da sallamarta.
Sororo tayi tana kallonta, “kai Zainab daga ina kike hakan kika baro mijinki cikin daren nan kika zo shiga hakk’in nawa Miji?, kuma fa kinsan cewa wannan lokacin bani bawa kowa shi sai Baban Iman”.
“Haba abin har da kora K’awata, naga fa kinci kwalliya kin gama aikinki yanzu da Maigidan ya dawo akaci abinci sai hira da kwanciya, ko fita za kuyi ne naga kinci kwalliya hakan?”.
“Ni kikasan cewa ina fita bayan magrib?, ai duk yawo na to da rana ne Baban Iman yana office, kan ya dawo niko na dawo daga unguwa nayi girki na gama”.
Suna cikin hakan ne suka ji hon na dawowar Baban Iman, Bahijja ce ta rik’a hannun Zainab tace ko ki tashi kiyi gidanki ko ki koma part (ɓangare na) ki zauna har in gama taryon maigidana”.
Fuska ta haɗe kana tace’ “wallahi bazan shiga gidan ba yanzu, waccan sarkin iyayin na can tana shirin tarairayar miji, bazan zauna bak’in ciki ya nemi salwantarda ni ba wallahi”.
Wani mugun kallo ta bita dashi tana mai girgiza kai kana ta turata ɓangarenta sannan ta fita ta taryo Baban Iman inda suka haɗu a falon. Da saurinta ta k’araso zata rungumeshi ya juya ya bata baya, gabanshi ta koma ta durk’usa tana mai rik’e da kunnenta alamar ban hak’uri, murmushi yayi yana mai rik’o hannunta ta mik’e tsaye.
“Me yasa kina jin horn ɗina yau bakije get kika taryoni ba?”.
“Sorry Baban Iman wallahi Zainab ce tazo shiyasa, inata sauri sai gashi har ka shigo falon”.
Tana kai k’arshen magana ta rik’a hannunshi suka yi ɓangarenshi, sai da ta haɗa mashi ruwan wankan ya shiga sannan ta zuzzuba abincin saboda yaɗan huce akan Baban Iman ba gwanin cin abinci mai zafi sosai bane.
Da fitowarshi ta ɗauki shawul tana mai taya shi tsane jikinshi, sannan ta bashi kayanshi marasa nauyi ya saka suka zauna suna cin abincin.
“Bak’uwarki ta wuce kenan?”.
“La haula kaga wallahi na manta da ita”.
Ido yaɗan zaro yace’ “je ku gama da ita, kar taga kin mata wulak’anci, ɗaukomin Iman ta tayani hira kan ku gama”.
“Iman ta gama rigima fa ta yi bacci”.
Laptop ɗinshi ya janyo yace’ “to kije na baki minti 30 zuwa lokacin nasan na k’arasa wani aiki”.
Sumba ta kai mashi tana godiya kana ta fice zuwa ɓangarenta. Zaune ta tarar da Zainab tana ƙlatsar waya tana sakin hamma. “Ga alama dai kishi ko abincin bai barki kika tsaya ci ba ko?”.
“Wallahi kamar kin sani, ke fa da mun zauna cin abinci zaki ga tana wani iyayi ita a dole ga mai Miji, don haka ni gaskiya ma na soke wannan zaman cin abinci tare, ranar girkinta su haɗu da yaransu ni ko ranar nawa girki abarni da Mijina”.
Abinci ta tashi ta sako mata sannan ta nemi guri gefenta ta zauna, “wai ni zainab na tambayeki, har yaushe kika san daɗin Mijin da kike kishi da Uwargidanki hakan?”.
Sai da ta saka lomar abinci a bakinta tace’ “wallahi baki ga shi kanshi rawar kan da yake akanta ba, dole ko kece kiji zafi”.
Murmushi tayi sannan tace’ “irinku ne masu fatan in sun shigo a gida Uwargida ta zamo abar tausayi a dinga nuna rawar kai a kanku ku gaku amare ko?”.
“To wallahi tun wuri ki canja wannan bak’ar ak’idar taki, yanzu ki k’iyasta akanki ace kece uwargidar aka yiwa kishiya miji ya sauya maki zaki ji daɗi?”.
Kai ta girgiza sannan tace’ “to amma sunyi nasu lokaci ya kamata yanzu abarni naci nawa”.
“Ok inna fahimce ki so kike taja gefe ta bar maki miji hannunki ita tace duk ta tsufa da kula da mijinta, kuma ta gaji da bautar ubangiji ke kije ki kwashe ladar?”.
“Ni fa bance ba”.
“To miye nufinki akai mai son miji?”.
“Kawai dai ta rage saboda kinga yanzu nice Amaryar kuma….”.
Saurin taryar numfashinta tayi sannan tace’ “wannan duk zancen banzane kike yi baki da makama ko rabi ballantana ɗaya, ni kinganni nan ko jikanyata aka yiwa aure k’arewar tsufa indai ina numfashi a doron k’asa bazan k’i bawa Mijina kulawa ba”.
“Wannan bak’ar ak’idar taki irinta ce ke tsorata uwargida muddin yace zai yi aure, bawai kishiyarce basa so ba a’ah bak’ar ak’idar da zata zo masu da ita ne basa so, saboda wasu da kaga yanda kansu ke rawa kasan da biyu suka shigo gidan, ko su fitar da kishiyar ko ta zamo shara a gidan”.
“Amma in har amarya tazo da niyyar alk’hairi to zaki ga zama yayi daɗi ana mutunta juna, saɓoda ba wanda ya shiga sabgar wani, kowa k’ok’arinshi ya kyautatawa Mijin dai_dai k’ima yanda zai samu gurbi a zuciyar maigidan, wannan shine kishi na asali, saboda haka don Allah ki ɗauke idonki akanta da yaranta, ki daina kula dame take yi har abin na damunki”.
“Abinda nake so ki kula dashi anan shine, misali ace in kuka zauna cin abinci ita Maman Farha saka mai abincin take yi yaci da kanshi, to ke sai ki kwatanta bashi a baki, in ruwa wanka take kai mashi ta fito to ke ki dinga taya shi da sauransu, ta hakan kishin y’an zamani da suka san kansu suke yi ba irin yanda kike yi ba, saboda haka don Allah ki gyara wannan halin naki”.
Shiru tayi alamar duk wani zance nata na shigarta da kyau, “insha Allah zan gyara, kuma nagode sosai da shawara Allah yabar zumunci”.
“Ba komai zaman tare ne, in kin ɗauka ta hakan ma zan samu nawa kason lada, don haka tashi kiyi gidanki ni zan shiga wanka inje mu kwanta ni da oga”.
“Wanka fa Bebeelo, yanzu fa na shiga na ganki da kwalliyarki kuma har wani wankan zakiyi? Bakya tsoron murar zafi ne gata da shegen kamu?”.
“Kina nufin yanzu hakan sai naje na rungumi Mijin hakan ina bashi_bashin zufa?, ai koke kika ga zan aikata hakan kya yimin faɗa Zainab”.
Zurum ta yi na y’an dak’ik’ik’i ta shiga dogon nazari akai. Bebeelo ce ta taɓota tace’ “Zainab lafiya?, ni fa kinga a cikin lokacinda Baban Iman ya bani saura minti bakwai, kuma wallahi yana cika zan ware na barki ne in kin fita kija min k’ofa”, ta k’arasa maganar tana murmushi.
“Maganarki ce ta sakani shiga wani nazari yanzun nan, saboda ni dai wallahi a yini wanka ɗaya nake yi kuma shine har dare in zamu kwanciya”.
“Suɓhanalillah!, Zainab kanki ɗaya kuwa, wane irin wanka ɗaya kina matar aure kuma a cikin CANJIN YANAYIN nan na zafi ace kina wanka ɗaya kije ki rungumi miji a hakan, wallahi ko Abban Farha ya zama ɗan halak daya juri zama dake shekara biyu a hakan”.
“To bara kiji wallahi ko ni da nake mace zamanin ina makaranta bana iya jurar zama kusa da k’azamai musamman lokacin, ashe ke felek’e ne kawai kike yi bakisan ma kan zama da Miji ba har kike kishin uwargidanshi”.
“Ba mamaki kwanaki kika zomin nan da wani banzar k’orafi naki wai Mijnku bai damu da kiss da romance ba, tun kina nuna mishi ra’ayinki kika ga baya yi kika hak’ura, a hakan zai iy haɗa baki dake tun brush ɗin safe har lokacin kwanciya, haba Zainab ina ilminki yake, ina wayewarki ina iyayenki da y’anuwanki abokanai na k’urciya da basu zamo makaranta a gareki ba?”.
Idon Zainab ne ya ciko da k’walla ta fara raina kanta da muzanta a idon Bebeelo.
“Ki saki ranki muyi magana ta fahimta saboda bama ɓoyewa juna abu na k’aruwa a tsakaninmu. Ki k’iyasta ke da kanki kiga in har kikayi wankan jikinki zakiji iska na shigarki ta ko ina kuma zakiji jikinki ya cire bashi musamman lokacin zafi”.
Muje zuwa.✍🏻


SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "CANJIN YANAYI 5"

Post a Comment