INA DA BURI kashi na 3
INA DA BURI
3
FEENAT JAFAR
&
HAFSA ISMA’IL(MMN
HANEEP).
3_Washegari sai baza ido take taji ance an fasa aure shiru,sai ma shiri da kowa taga yana yi baki a washe.
3_Washegari sai baza ido take taji ance an fasa aure shiru,sai ma shiri da kowa taga yana yi baki a washe.
Gabanshi ta sha ganin
yana neman fita tana dan satar kallonshi ganin sosai yau yai kyau tamkar ango.
“Ina kwana..
“Ina kwana..
A ciki-ciki ta gaida
shi,murmushi yai tare da hard’e hannu yana kallonta.
Baki ta zumburo jin
yai mata banza da wannan munafukin murmushin nashi,dan haka sai ta hau yatsina
tana fad’in
“Ni fa ban gane ba,koh ka fasa taimakon nawa naga kowa na shiri?
“Ni fa ban gane ba,koh ka fasa taimakon nawa naga kowa na shiri?
Tsayuwa ya gyara yana
kallonta,dan haka tuni ta sake kulewa.
“Ladabi shi yai miki
karanci..
Rai tai saurin had’e
wa tare da mishi kallon sama da kasa cike da kar ka rainan hankali..
Ajiyar zuciya ya yi tare daga kafad’a
Ajiyar zuciya ya yi tare daga kafad’a
“Koh da yake,kar kiji
komai,na gama taimakon ki tunda kin roka jiya,ki sa ido babu aurenki da Najib
Insha-Allah..
Fuska ta saki ganin ya
juya ta sake yin saurin shan gabanshi,Abba da ya sakko yana kallon yadda take farin
ciki,hala koh ta san abinda ke gudana?
Murmushi ya yi ganin yadda Kamal din ma yake mata murmushi har ya fuce.
Murmushi ya yi ganin yadda Kamal din ma yake mata murmushi har ya fuce.
Juyo wa tai,da mamakin
shi harda gaidashi ta shige d’aki,ita fa a dole sunyi wa Abba wayo.
Ta sani Kamal in ya ce
toh ya ce,bai da karya a lamuranshi,dan haka tasan aure babu.
Da kallo kawai Mamy ke binta ganin yadda take rawar kan,sai ta girgiza kai da murmushin mugunta,tasan karyar y’arta kam ta kare.
Da kallo kawai Mamy ke binta ganin yadda take rawar kan,sai ta girgiza kai da murmushin mugunta,tasan karyar y’arta kam ta kare.
Dan haka da ido kawai
take binta.
Kasantuwar aure babu wani shiri yasa gidan ba jama’a sosai,har kawayenta ta ce kar wanda yazo.
Kasantuwar aure babu wani shiri yasa gidan ba jama’a sosai,har kawayenta ta ce kar wanda yazo.
Kasantuwar a unguwar
Baba Zubairu ake taro bata san wainar da ake toya wa ba sai da suka dawo kusan
sha biyun rana.
Tana d’akin Mamy sai alkawari take mata akan Insha-Allah ta kusa samun cikar burinta tai mata adu’a kawai.
Tana d’akin Mamy sai alkawari take mata akan Insha-Allah ta kusa samun cikar burinta tai mata adu’a kawai.
Kai Mamyn ta kad’a
tana murmushi, kai daga gani na baki da wayo ne.
Yayunta ne suka shigo da sallama,kowa bakin nan har k’unne.
Yayunta ne suka shigo da sallama,kowa bakin nan har k’unne.
“Kun dawo?
Kai su ka jijjiga
“Eh Mamy.
Deeja su ka kalla tare
da fad’in
“Congratulations toh
Deeja…
Baki ta wage harda
fad’in
“Thanks..ina yaya
Kamal?
Leko wa yai yasha shadda fara ganin d’akin ya cika bai shigo ba.
Leko wa yai yasha shadda fara ganin d’akin ya cika bai shigo ba.
Hannu ta daga mishi
tare da fad’in
“Na gode
A hankali.
Kai ya karkatar
halamun u r welcome.
“Ai Najib Mamy yana
chan sai bori yake wai akan ba dashi aka d’aura ba sai da wani…
Da sauri ta kallo Salis wanda ke magana.
Da sauri ta kallo Salis wanda ke magana.
“Ban gane ba?
Kallonta su kai ganin
yadda ta sa mishi ido.
“Kwarai, ba’a d’aura
da Najib ba,na cikin gida akai..
Ido ta zaro tare da
fad’in
“Waye wani?
“A ina yake?
“Kamal man,waye na cikin gida in ba shi ba…
“Kamal man,waye na cikin gida in ba shi ba…
Kamal din ta kallo da
sauri cike da tuhumar haka mukai da kai? Tana had’iye wani d’ad’d’acen yawu
jiki na ka’rkarwa,a zabure zatai kanshi taji ta kasa motsi ganin yana mata
murmushin mugunta,kan ta farga har ta fara ganin duhu.
A hankali ta fara tangad’i kowa hankalinshi yai kan Mamy su na mata dariyar keta,luu ta tafi zata fad’i da azama ya turo ciki tare da rukota.
A hankali ta fara tangad’i kowa hankalinshi yai kan Mamy su na mata dariyar keta,luu ta tafi zata fad’i da azama ya turo ciki tare da rukota.
“Deeja..
Gaba d’aya suka
kallosu har Mamy jin kiran da Kamal d’in ke mata suka rufa kanta.
Jijjigata su ke,sai
dai Deeja ba sauran numfashi.
“Mamy fa suma tai inaga..
“Mamy fa suma tai inaga..
Cicci6arta ya yi tare
da d’aurata gadon Mamy Zaid ya tafi fridge dan d’akko ruwa sai ganan sun shigo
shi da Abba a sukwane.
“Ku matsa,garin yaya
ta suma?
Kauce wa sukai Abban
ya hau gadon,yayyafawar ruwan duniya Deeja taki motsi dan haka dole su ka
danganta da asibiti.
Yasan tai nisa a suman da tai dan likitoci sun tabbatar shock ne ya jawo mata haka anjima kad’an zata farfad’o.
Yasan tai nisa a suman da tai dan likitoci sun tabbatar shock ne ya jawo mata haka anjima kad’an zata farfad’o.
Kowa yai jigum ana
jiran tsammanin tashin Deeja.
Gida suka tafi jin
numfashinta ya dawo normal amma sun mata allurar bacci.
Kamal ke kanta dasu Mamy a waje.
Kamal ke kanta dasu Mamy a waje.
Ido ta fara juya wa da
kok’arin zata bud’e su dan haka sai ya matso yadda in ta bud’e ta fara
kallonshi.
Warai ta bud’e dan
tuno da abinda ya faru dazun tare da kallon d’akin, akanshi idonta ya sauka.
Hannu ya dago mata halamun hi! Yana murmushi mugunta.
Hannu ya dago mata halamun hi! Yana murmushi mugunta.
“Kin tashi?
Ido ta sa mishi tana
mai tunano abinda da ya faru.
“Ba suma ba ai koh
mutuwa ki ke kina dawo wa dole ki kar6i taimako na..
A zabure ta tashi daga kan pillown tana dafe kai jin komai ya dawo mata,a take ta fara yarfo mishi ruwan bala’i
A zabure ta tashi daga kan pillown tana dafe kai jin komai ya dawo mata,a take ta fara yarfo mishi ruwan bala’i
“Wallahi Allah ya isa
bazan ta6a yafe maka mugun kawai maketaci,dama wannan ne taimakon naka? Toh
wallahi baka isa ba,dole ka sake ni..
Dariya ya fara irin wacce bata ma san ya iyata ba,dan irin ta ketar nan harda rike ciki.
Dariya ya fara irin wacce bata ma san ya iyata ba,dan irin ta ketar nan harda rike ciki.
Dan tsabar takaici
kawai sai ta sau mishi kuka tana mai sake maimaita Allah ya isa ba iyaka yana
dariya.
0 Response to "INA DA BURI kashi na 3"
Post a Comment