INA DA BURI kashi na 3

INA DA BURI
3
FEENAT JAFAR
          &
HAFSA ISMA’IL(MMN HANEEP).
3_Washegari sai baza ido take taji ance an fasa aure shiru,sai ma shiri da kowa taga yana yi baki a washe.
Gabanshi ta sha ganin yana neman fita tana dan satar kallonshi ganin sosai yau yai kyau tamkar ango.
“Ina kwana..
A ciki-ciki ta gaida shi,murmushi yai tare da hard’e hannu yana kallonta.
Baki ta zumburo jin yai mata banza da wannan munafukin murmushin nashi,dan haka sai ta hau yatsina tana fad’in
“Ni fa ban gane ba,koh ka fasa taimakon nawa naga kowa na shiri?
Tsayuwa ya gyara yana kallonta,dan haka tuni ta sake kulewa.
“Ladabi shi yai miki karanci..
Rai tai saurin had’e wa tare da mishi kallon sama da kasa cike da kar ka rainan hankali..
Ajiyar zuciya ya yi tare daga kafad’a
“Koh da yake,kar kiji komai,na gama taimakon ki tunda kin roka jiya,ki sa ido babu aurenki da Najib Insha-Allah..
Fuska ta saki ganin ya juya ta sake yin saurin shan gabanshi,Abba da ya sakko yana kallon yadda take farin ciki,hala koh ta san abinda ke gudana?
Murmushi ya yi ganin yadda Kamal din ma yake mata murmushi har ya fuce.
Juyo wa tai,da mamakin shi harda gaidashi ta shige d’aki,ita fa a dole sunyi wa Abba wayo.
Ta sani Kamal in ya ce toh ya ce,bai da karya a lamuranshi,dan haka tasan aure babu.
Da kallo kawai Mamy ke binta ganin yadda take rawar kan,sai ta girgiza kai da murmushin mugunta,tasan karyar y’arta kam ta kare.
Dan haka da ido kawai take binta.
Kasantuwar aure babu wani shiri yasa gidan ba jama’a sosai,har kawayenta ta ce kar wanda yazo.
Kasantuwar a unguwar Baba Zubairu ake taro bata san wainar da ake toya wa ba sai da suka dawo kusan sha biyun rana.
Tana d’akin Mamy sai alkawari take mata akan Insha-Allah ta kusa samun cikar burinta tai mata adu’a kawai.
Kai Mamyn ta kad’a tana murmushi, kai daga gani na baki da wayo ne.
Yayunta ne suka shigo da sallama,kowa bakin nan har k’unne.
“Kun dawo?
Kai su ka jijjiga
“Eh Mamy.
Deeja su ka kalla tare da fad’in
“Congratulations toh Deeja…
Baki ta wage harda fad’in
“Thanks..ina yaya Kamal?
Leko wa yai yasha shadda fara ganin d’akin ya cika bai shigo ba.
Hannu ta daga mishi tare da fad’in
“Na gode
A hankali.
Kai ya karkatar halamun u r welcome.
“Ai Najib Mamy yana chan sai bori yake wai akan ba dashi aka d’aura ba sai da wani…
Da sauri ta kallo Salis wanda ke magana.
“Ban gane ba?
Kallonta su kai ganin yadda ta sa mishi ido.
“Kwarai, ba’a d’aura da Najib ba,na cikin gida akai..
Ido ta zaro tare da fad’in
“Waye wani?
“A ina yake?
“Kamal man,waye na cikin gida in ba shi ba…
Kamal din ta kallo da sauri cike da tuhumar haka mukai da kai? Tana had’iye wani d’ad’d’acen yawu jiki na ka’rkarwa,a zabure zatai kanshi taji ta kasa motsi ganin yana mata murmushin mugunta,kan ta farga har ta fara ganin duhu.
A hankali ta fara tangad’i kowa hankalinshi yai kan Mamy su na mata dariyar keta,luu ta tafi zata fad’i da azama ya turo ciki tare da rukota.
“Deeja..
Gaba d’aya suka kallosu har Mamy jin kiran da Kamal d’in ke mata suka rufa kanta.
Jijjigata su ke,sai dai Deeja ba sauran numfashi.
“Mamy fa suma tai inaga..
Cicci6arta ya yi tare da d’aurata gadon Mamy Zaid ya tafi fridge dan d’akko ruwa sai ganan sun shigo shi da Abba a sukwane.
“Ku matsa,garin yaya ta suma?
Kauce wa sukai Abban ya hau gadon,yayyafawar ruwan duniya Deeja taki motsi dan haka dole su ka danganta da asibiti.
Yasan tai nisa a suman da tai dan likitoci sun tabbatar shock ne ya jawo mata haka anjima kad’an zata farfad’o.
Kowa yai jigum ana jiran tsammanin tashin Deeja.
Gida suka tafi jin numfashinta ya dawo normal amma sun mata allurar bacci.
Kamal ke kanta dasu Mamy a waje.
Ido ta fara juya wa da kok’arin zata bud’e su dan haka sai ya matso yadda in ta bud’e ta fara kallonshi.
Warai ta bud’e dan tuno da abinda ya faru dazun tare da kallon d’akin, akanshi idonta ya sauka.
Hannu ya dago mata halamun hi! Yana murmushi mugunta.
“Kin tashi?
Ido ta sa mishi tana mai tunano abinda da ya faru.
“Ba suma ba ai koh mutuwa ki ke kina dawo wa dole ki kar6i taimako na..
A zabure ta tashi daga kan pillown tana dafe kai jin komai ya dawo mata,a take ta fara yarfo mishi ruwan bala’i
“Wallahi Allah ya isa bazan ta6a yafe maka mugun kawai maketaci,dama wannan ne taimakon naka? Toh wallahi baka isa ba,dole ka sake ni..
Dariya ya fara irin wacce bata ma san ya iyata ba,dan irin ta ketar nan harda rike ciki.
Dan tsabar takaici kawai sai ta sau mishi kuka tana mai sake maimaita Allah ya isa ba iyaka yana dariya.


SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "INA DA BURI kashi na 3"

Post a Comment