INA DA BURI Kashi na 5
*INA DA BURI 5*
FEENAT JAFAR
&
HAFSA ISMA’IL(MMN
HANEEP).
5_Ba koh sallama aka bankad’o kofar d’akin nasu sai huci take kamar ta ci babu.
5_Ba koh sallama aka bankad’o kofar d’akin nasu sai huci take kamar ta ci babu.
Ido ya sa mata
fuskarshi ba yabo ba fallasa,har mamakin zuciyarshi yake in ya tuno wai tana
kwadaituwa da son Deeja.
Yarinya da ciwan kanta
ma a ganinshi bata sani ba balle tasan na wani.
Ya sani a in da wanda Deeja taki jinin gani a yanzu toh bai wuce shi ba,dan tana mishi tsanar da k’arara kowa ke iya ganinta kwance bisa fuskanta.
Ya sani a in da wanda Deeja taki jinin gani a yanzu toh bai wuce shi ba,dan tana mishi tsanar da k’arara kowa ke iya ganinta kwance bisa fuskanta.
Murmushi ya yi a
zuciyarshi, abu daya ne bata sani ba,aurenshi da ita shi ake kira *Mutu ka
raba, wai takalmin kaza*.
***
Fushi ta diba yi da kowa cikin gidan har Abba,dan ya sake jaddada mata hukuncin shi na nan bisa kanta.
Fushi ta diba yi da kowa cikin gidan har Abba,dan ya sake jaddada mata hukuncin shi na nan bisa kanta.
Ba ruwanta da sha’anin
kowa,kamar yadda kowa ya d’auke mata wuta,abinci sai ta ga dama zata ci.
Kusan wata guda kenan da auren,dan haka Abba ya ce su tattara a tare haka nan kila in ta bar gida zata saduda.
Kusan wata guda kenan da auren,dan haka Abba ya ce su tattara a tare haka nan kila in ta bar gida zata saduda.
Ranar taci kuka jin da
gaske zata tare gidan Kamal.
Kamal d’in ne ya samu
Abba da zancen kaita garin su.
“Abba ina son muje chan Kogar gun Abba kamin..
“Abba ina son muje chan Kogar gun Abba kamin..
Kai ya dan sosa yana
sinke kai,dan haka sai Abban ya kad’a kai yana murmushi.
“Ai munyi waya na
sanarshi komai,dan haka ka tafi da iyalin naka chan dan su santa.
Kai ya sake duk’arwa
yana godiya.
Deejan ya kwad’a ma kira,chan ciki ta amsa tare da fito wa tana chunno baki a dole ita fushi take dashi.
Deejan ya kwad’a ma kira,chan ciki ta amsa tare da fito wa tana chunno baki a dole ita fushi take dashi.
“Ki kimtsa za ki bi
mijinki ya nuna miki ‘yan uwa kamin ku tare chan Kogar da sauran su.
Kai ta dago da sauri tana kallon Abban kamar ta sau kuka,dan haka sai Kamal din ya basu waje.
Kai ta dago da sauri tana kallon Abban kamar ta sau kuka,dan haka sai Kamal din ya basu waje.
“Khadija..
Nan a ciki ta amsa.
“Na baki dukkanin wani
so da kulawa,ban ta6a neman wata alfarma a gareki ba sai wannan.
“Ki min alfarmar yi wa aurenki biyayya,kar ki bani kunya in kunje gun abokina koh danginshi..
“Ki min alfarmar yi wa aurenki biyayya,kar ki bani kunya in kunje gun abokina koh danginshi..
Jinshi take kawai har
ya gama,ita tunaninta ya ma zata iya rayuwa cikin kauyen su Kamal koh ta yini
ne,dan haka ba komai taji ba illa tunanin abinda zata riska.
***
A Kogar.
Kallon kowa take a raine, duk da su sun mata tar6ar kirki da karamci barin su Badiyya k’anwar Kamal.
A Kogar.
Kallon kowa take a raine, duk da su sun mata tar6ar kirki da karamci barin su Badiyya k’anwar Kamal.
Duk ido ya sa mata
yana karantar ta,hatta abinci taki ci sai yatsine fuska take halamun ta raina
muhallinsu.
Tunani take yanzu kila wannan matar har ita auren Baban Kamal ya kusa sittin..
Tunani take yanzu kila wannan matar har ita auren Baban Kamal ya kusa sittin..
Kai ta girgiza,
“A’a na barshi a
talatin..
Nutsuwa tai tare da
kallon ko’ina, d’aki ne na kasa yasha leda sabuwa ko’ina kal-kal.
Baki ta dan ta6e,duk yana kallonta ta window.
Baki ta dan ta6e,duk yana kallonta ta window.
Kai ya jijjiga tare da
shiga d’akin.
Rai tai saurin had’ewa
tare da mike wa.
“Na fa sanar ka ni ban
son shisshigi ka rika yin nesa-nesa dani da inda nake.
A raine yake kallonta,
chan dai ya jijjiga kai tare da fad’in
“Ki shirya gobe riga zamu dama,da sannu zan karad’e miki kauye nah kamar yadda Abba ya ce.
“Ki shirya gobe riga zamu dama,da sannu zan karad’e miki kauye nah kamar yadda Abba ya ce.
Harara ta maka
mishi,sai ya jijjiga kai ya fuce.
***
Kwanan su d’aya a Babban gida washegari ranar kasuwa ya samu ‘yan uwan Mamanshi sunzo cin kasuwa dan haka tare zasu bisu.
Kwanan su d’aya a Babban gida washegari ranar kasuwa ya samu ‘yan uwan Mamanshi sunzo cin kasuwa dan haka tare zasu bisu.
Ido ta zaro ganin
motar da ake d’anewa wai nan zata hau.
Da hannu ta nuno mishi
motar.
“Wai kana nufin a wannan akori kurar motar zamu tafi?
“Wai kana nufin a wannan akori kurar motar zamu tafi?
Kai ya d’auke tare da
sanya jakar su,
“Malam da fa kai
nake..
“Ki jira sai na miki
bayani.
Motar ya d’ane kamar
yadda yaga sauran sunyi ya batta baki sake tana sake karewa buddadiyar motar
kallo.
Masifa ta fara a kan fafur sai ya sauke mata kayanta dan fa ba ta6a hawa ba,ba kuma zata hau ba.
Masifa ta fara a kan fafur sai ya sauke mata kayanta dan fa ba ta6a hawa ba,ba kuma zata hau ba.
Kai ya jijjiga
“Toh ki san inda dare
ya miki tun wuri..
Harara ta galla mishi
tare da rike k’ugu tana masifar dole ne sai taje?.
Jin mota na dirin
tashi ga wasu gunguma gunguman shanu na taho wa yasa ta fara raba ido.
Banza yai mata har aka tada mota,
Banza yai mata har aka tada mota,
“Toh ta ina zan hau?
Juyo wa yai tare da
kallonta,kan ta aune har ya sau dariya.
Dakyar ta iya hawa
shima sai da ya taimaka mata.
Tafiya akai mai d’an
nisa tana gani ya tushe rabin fuskarshi.
Sosai yau ta jigata, harda kukanta lokacin da za a sauka taga wai ba’a zo ba an tsayarda babur wai mota bata shiga wajen.
Sosai yau ta jigata, harda kukanta lokacin da za a sauka taga wai ba’a zo ba an tsayarda babur wai mota bata shiga wajen.
Haka tana ji tana gani
ta d’ane babur ga magriba ta sanyo kai sai dariyar keta yake mata.
Duhu cur suka isa rigar Mongwano,ga bakar yunwa,ga gajiya,tun kan aje ko’ina har ta tantance Kogar babban birni akan nan ganin yadda take cin karo da bukka.
Duhu cur suka isa rigar Mongwano,ga bakar yunwa,ga gajiya,tun kan aje ko’ina har ta tantance Kogar babban birni akan nan ganin yadda take cin karo da bukka.
Cikin yaren fillanci
suka kewaye su da fitulu cike da murnar zuwan Kamalu.
A jigace ta kalloshi,
A jigace ta kalloshi,
“Ruwa..
Ido ya sa mata,tun kan
aje ko’ina har ta shiga hankalinta.
A ‘yar karamar kwarya
aka kawo mata ruwan dan haka kawai sai ta daga ta hau kwankwad’a.
Tasha kusan rabi taji
ina ba gama ga wani karni da ruwan yake.
Sauke wa tai tare da haska shi.
Sauke wa tai tare da haska shi.
Gaba d’aya bai mata
kalar ruwa ba,yafi kama da lamurje,dan haka da sauri ta ajiye tare da fara
yatsine fuska kamar tai amai.
Kai ya jijjiga, yana
auna bata ma ga komai ba..
Abinci kuwa loma d’aya ta cire hannu tana kallonshi yadda yake shan nono.
Abinci kuwa loma d’aya ta cire hannu tana kallonshi yadda yake shan nono.
Harara ta galla mishi
tare itama d’auka ta ture abincin.
Kur6a d’aya tai saurin
furzarwa jin tai karo da tsami da wani dogon abu.
Nonon ta haska,sam ba
irin na gari bane duk ba kyan gani.
A marairaice ta kalloshi jin yadda yake sakar dariyar keta.
A marairaice ta kalloshi jin yadda yake sakar dariyar keta.
“Amma dai dama kashe
ni kazo yi garin nan koh?
A dirare ya kallota ba
kiftawa,kan ta farga ya sake ke cewa da dariya.
“Welcome to Mongwano
city..
Kuka ta saka mishi
cike da jigata ga yunwa.
“Yarinya baki ga komai ba ma,a gaba akwai inda zamu koh wannan din ma ba zaki samu ba..
“Yarinya baki ga komai ba ma,a gaba akwai inda zamu koh wannan din ma ba zaki samu ba..
Baki ta ta6e tana mai
sake artayo kukanta har mutanen gidan su ka fito ganin koh lafiya.
Lalle yau ta sake
yadda da bakar muguntar Kamal mai yawa ce.
Da fillanci yai musu magana,dan haka sai d’aya ya koma tare da dakko mata kosai da fanken da ya siyo a kasuwar Babban guda ya bata su na mata dariya da fulanci.
Da fillanci yai musu magana,dan haka sai d’aya ya koma tare da dakko mata kosai da fanken da ya siyo a kasuwar Babban guda ya bata su na mata dariya da fulanci.
Dama-dama, dan haka
tana ji tana gani wannan taci yana ta kela mata dariyar mugunta.
Gado aka bata a cikin ‘yar dukurkurar bukkar wanda sai ta tsuguna take tsayuwa.
Gado aka bata a cikin ‘yar dukurkurar bukkar wanda sai ta tsuguna take tsayuwa.
Ajiyar zuciya ta sau
tare da kallon ‘yan matan dake gulmarta su na kunshe dariya.
Kaya ta cire tare da
sanya na bacci ta daura zani a kai.
Zani ta sake shimfida
wa bisa gadon jin yadda yake sukarta tamkar da kaya akayi shi.
Chan taji abu na dan zubo mata bayan ta kwanta.
Chan taji abu na dan zubo mata bayan ta kwanta.
Waya ta haska tana
tsaki a zatonta koh kasa ce.
Wasu k’ananan kwari ne
da gara ashe da wasu bak’ak’e suke zubo wa daga sama.
Baki ta ta6e da zummar sakar kuka dan bakin ciki,ina wai Kamal ya kawo ta?
Baki ta ta6e da zummar sakar kuka dan bakin ciki,ina wai Kamal ya kawo ta?
Gyalenta ta dakko tare
da lullu6a tana tsaki ita kad’ai tare da kallo y’an matan da suka kwanta abin
su.
Abu taji yana yawo
bisa kanta a saman gyalen,dan haka tuni ta fara raba ido tare da janyo waya a
hankali.
Gyalen ta yaye tare da haska wa,wata bakar katuwar kunama ce ta daga kari sama,da karfi ta yar da gyalen tare da dira a gadon ta ari na kare ta fuce tana ihu
Gyalen ta yaye tare da haska wa,wata bakar katuwar kunama ce ta daga kari sama,da karfi ta yar da gyalen tare da dira a gadon ta ari na kare ta fuce tana ihu
“Wayyo kunama…
Tashi yai tare da saurin
zuwa inda take kukan,tana ganinshi ta rukunkumeshi tare da fad’in
“Wallahi bazan kwanta a d’akin nan ba..
“Wallahi bazan kwanta a d’akin nan ba..
Mutanen gidan ne suka
fito jin ihun nata.
Hannu ya kai kan
bak’inshi yana fad’in
“Shshhh,to anji, bata
cije ki bade koh?
Kai ta daga da sauri
tana maida numfashi.
Fur taki koma
wa,karshe inda ya kwanta da Buba nan ya ra6a mata ta raka6e daga zaune shi kuma
ya shige makwancinshi.
Yadda take rike da hannunshi kam yasa ya sa mata ido,yau d’aya har ta dawo abin tausayi.
Yadda take rike da hannunshi kam yasa ya sa mata ido,yau d’aya har ta dawo abin tausayi.
“Ki ma ware,dan sati
muka zo yi a nan.
Ido ta zaro tare da
marairaice fuska,da sauri ta hau burburwa fad’i take
“Wallahi baka isa ba
gobe zan bar garin nan.
Kai ya girgiza tare da fad’in
Kai ya girgiza tare da fad’in
“Toh mu zuba,ai sai
randa naga kinyi ladab.
Ranar kam tasha kuka
da kiran Mamy,tasan in tai sati a garin nan kila sai dai a d’au gawarta.
Karyar raina mishi
muhalli yasan ta kare.
0 Response to "INA DA BURI Kashi na 5"
Post a Comment