INA DA BURI Kashi na 5

 *INA DA BURI   5*
FEENAT JAFAR
          &
HAFSA ISMA’IL(MMN HANEEP).
5_Ba koh sallama aka bankad’o kofar d’akin nasu sai huci take kamar ta ci babu.
Ido ya sa mata fuskarshi ba yabo ba fallasa,har mamakin zuciyarshi yake in ya tuno wai tana kwadaituwa da son Deeja.
Yarinya da ciwan kanta ma a ganinshi bata sani ba balle tasan na wani.
Ya sani a in da wanda Deeja taki jinin gani a yanzu toh bai wuce shi ba,dan tana mishi tsanar da k’arara kowa ke iya ganinta kwance bisa fuskanta.
Murmushi ya yi a zuciyarshi, abu daya ne bata sani ba,aurenshi da ita shi ake kira *Mutu ka raba, wai takalmin kaza*.
***
Fushi ta diba yi da kowa cikin gidan har Abba,dan ya sake jaddada mata hukuncin shi na nan bisa kanta.
Ba ruwanta da sha’anin kowa,kamar yadda kowa ya d’auke mata wuta,abinci sai ta ga dama zata ci.
Kusan wata guda kenan da auren,dan haka Abba ya ce su tattara a tare haka nan kila in ta bar gida zata saduda.
Ranar taci kuka jin da gaske zata tare gidan Kamal.
Kamal d’in ne ya samu Abba da zancen kaita garin su.
“Abba ina son muje chan Kogar gun Abba kamin..
Kai ya dan sosa yana sinke kai,dan haka sai Abban ya kad’a kai yana murmushi.
“Ai munyi waya na sanarshi komai,dan haka ka tafi da iyalin naka chan dan su santa.
Kai ya sake duk’arwa yana godiya.
Deejan ya kwad’a ma kira,chan ciki ta amsa tare da fito wa tana chunno baki a dole ita fushi take dashi.
“Ki kimtsa za ki bi mijinki ya nuna miki ‘yan uwa kamin ku tare chan Kogar da sauran su.
Kai ta dago da sauri tana kallon Abban kamar ta sau kuka,dan haka sai Kamal din ya basu waje.
“Khadija..
Nan a ciki ta amsa.
“Na baki dukkanin wani so da kulawa,ban ta6a neman wata alfarma a gareki ba sai wannan.
“Ki min alfarmar yi wa aurenki biyayya,kar ki bani kunya in kunje gun abokina koh danginshi..
Jinshi take kawai har ya gama,ita tunaninta ya ma zata iya rayuwa cikin kauyen su Kamal koh ta yini ne,dan haka ba komai taji ba illa tunanin abinda zata riska.
***
A Kogar.
Kallon kowa take a raine, duk da su sun mata tar6ar kirki da karamci barin su Badiyya k’anwar Kamal.
Duk ido ya sa mata yana karantar ta,hatta abinci taki ci sai yatsine fuska take halamun ta raina muhallinsu.
Tunani take yanzu kila wannan matar har ita auren Baban Kamal ya kusa sittin..
Kai ta girgiza,
“A’a na barshi a talatin..
Nutsuwa tai tare da kallon ko’ina, d’aki ne na kasa yasha leda sabuwa ko’ina kal-kal.
Baki ta dan ta6e,duk yana kallonta ta window.
Kai ya jijjiga tare da shiga d’akin.
Rai tai saurin had’ewa tare da mike wa.
“Na fa sanar ka ni ban son shisshigi ka rika yin nesa-nesa dani da inda nake.
A raine yake kallonta, chan dai ya jijjiga kai tare da fad’in
“Ki shirya gobe riga zamu dama,da sannu zan karad’e miki kauye nah kamar yadda Abba ya ce.
Harara ta maka mishi,sai ya jijjiga kai ya fuce.
***
Kwanan su d’aya a Babban gida washegari ranar kasuwa ya samu ‘yan uwan Mamanshi sunzo cin kasuwa dan haka tare zasu bisu.
Ido ta zaro ganin motar da ake d’anewa wai nan zata hau.
Da hannu ta nuno mishi motar.
“Wai kana nufin a wannan akori kurar motar zamu tafi?
Kai ya d’auke tare da sanya jakar su,
“Malam da fa kai nake..
“Ki jira sai na miki bayani.
Motar ya d’ane kamar yadda yaga sauran sunyi ya batta baki sake tana sake karewa buddadiyar motar kallo.
Masifa ta fara a kan fafur sai ya sauke mata kayanta dan fa ba ta6a hawa ba,ba kuma zata hau ba.
Kai ya jijjiga
“Toh ki san inda dare ya miki tun wuri..
Harara ta galla mishi tare da rike k’ugu tana masifar dole ne sai taje?.
Jin mota na dirin tashi ga wasu gunguma gunguman shanu na taho wa yasa ta fara raba ido.
Banza yai mata har aka tada mota,
“Toh ta ina zan hau?
Juyo wa yai tare da kallonta,kan ta aune har ya sau dariya.
Dakyar ta iya hawa shima sai da ya taimaka mata.
Tafiya akai mai d’an nisa tana gani ya tushe rabin fuskarshi.
Sosai yau ta jigata, harda kukanta lokacin da za a sauka taga wai ba’a zo ba an tsayarda babur wai mota bata shiga wajen.
Haka tana ji tana gani ta d’ane babur ga magriba ta sanyo kai sai dariyar keta yake mata.
Duhu cur suka isa rigar Mongwano,ga bakar yunwa,ga gajiya,tun kan aje ko’ina har ta tantance Kogar babban birni akan nan ganin yadda take cin karo da bukka.
Cikin yaren fillanci suka kewaye su da fitulu cike da murnar zuwan Kamalu.
A jigace ta kalloshi,
“Ruwa..
Ido ya sa mata,tun kan aje ko’ina har ta shiga hankalinta.
A ‘yar karamar kwarya aka kawo mata ruwan dan haka kawai sai ta daga ta hau kwankwad’a.
Tasha kusan rabi taji ina ba gama ga wani karni da ruwan yake.
Sauke wa tai tare da haska shi.
Gaba d’aya bai mata kalar ruwa ba,yafi kama da lamurje,dan haka da sauri ta ajiye tare da fara yatsine fuska kamar tai amai.
Kai ya jijjiga, yana auna bata ma ga komai ba..
Abinci kuwa loma d’aya ta cire hannu tana kallonshi yadda yake shan nono.
Harara ta galla mishi tare itama d’auka ta ture abincin.
Kur6a d’aya tai saurin furzarwa jin tai karo da tsami da wani dogon abu.
Nonon ta haska,sam ba irin na gari bane duk ba kyan gani.
A marairaice ta kalloshi jin yadda yake sakar dariyar keta.
“Amma dai dama kashe ni kazo yi garin nan koh?
A dirare ya kallota ba kiftawa,kan ta farga ya sake ke cewa da dariya.
“Welcome to Mongwano city..
Kuka ta saka mishi cike da jigata ga yunwa.
“Yarinya baki ga komai ba ma,a gaba akwai inda zamu koh wannan din ma ba zaki samu ba..
Baki ta ta6e tana mai sake artayo kukanta har mutanen gidan su ka fito ganin koh lafiya.
Lalle yau ta sake yadda da bakar muguntar Kamal mai yawa ce.
Da fillanci yai musu magana,dan haka sai d’aya ya koma tare da dakko mata kosai da fanken da ya siyo a kasuwar Babban guda ya bata su na mata dariya da fulanci.
Dama-dama, dan haka tana ji tana gani wannan taci yana ta kela mata dariyar mugunta.
Gado aka bata a cikin ‘yar dukurkurar bukkar wanda sai ta tsuguna take tsayuwa.
Ajiyar zuciya ta sau tare da kallon ‘yan matan dake gulmarta su na kunshe dariya.
Kaya ta cire tare da sanya na bacci ta daura zani a kai.
Zani ta sake shimfida wa bisa gadon jin yadda yake sukarta tamkar da kaya akayi shi.
Chan taji abu na dan zubo mata bayan ta kwanta.
Waya ta haska tana tsaki a zatonta koh kasa ce.
Wasu k’ananan kwari ne da gara ashe da wasu bak’ak’e suke zubo wa daga sama.
Baki ta ta6e da zummar sakar kuka dan bakin ciki,ina wai Kamal ya kawo ta?
Gyalenta ta dakko tare da lullu6a tana tsaki ita kad’ai tare da kallo y’an matan da suka kwanta abin su.
Abu taji yana yawo bisa kanta a saman gyalen,dan haka tuni ta fara raba ido tare da janyo waya a hankali.
Gyalen ta yaye tare da haska wa,wata bakar katuwar kunama ce ta daga kari sama,da karfi ta yar da gyalen tare da dira a gadon ta ari na kare ta fuce tana ihu
“Wayyo kunama…
Tashi yai tare da saurin zuwa inda take kukan,tana ganinshi ta rukunkumeshi tare da fad’in
“Wallahi bazan kwanta a d’akin nan ba..
Mutanen gidan ne suka fito jin ihun nata.
Hannu ya kai kan bak’inshi yana fad’in
“Shshhh,to anji, bata cije ki bade koh?
Kai ta daga da sauri tana maida numfashi.
Fur taki koma wa,karshe inda ya kwanta da Buba nan ya ra6a mata ta raka6e daga zaune shi kuma ya shige makwancinshi.
Yadda take rike da hannunshi kam yasa ya sa mata ido,yau d’aya har ta dawo abin tausayi.
“Ki ma ware,dan sati muka zo yi a nan.
Ido ta zaro tare da marairaice fuska,da sauri ta hau burburwa fad’i take
“Wallahi baka isa ba gobe zan bar garin nan.
Kai ya girgiza tare da fad’in
“Toh mu zuba,ai sai randa naga kinyi ladab.
Ranar kam tasha kuka da kiran Mamy,tasan in tai sati a garin nan kila sai dai a d’au gawarta. 
Karyar raina mishi muhalli yasan ta kare.


SUBSCRIBE TO OUR NEWSLETTER

Seorang Blogger pemula yang sedang belajar

0 Response to "INA DA BURI Kashi na 5"

Post a Comment