CANJIN YANAYI 3
©MARYAM ADAM
Sai da tayi wanka daga ɗakinta ta kimtsa sannan ta dawo ɗakin nashi, da
murnarshi ya taryota suka k’arasa gefen gadon. Ita kanta in tace ta samu CANJIN
YANAYI ta wannan ɓangaren to bata yiwa Kabeer adalci ba, sai dai ita a
tunaninta wace irin haɗama ce ke sanya maza tara mata dayawa, wata zuciyar ce
ta tunatar da ita cewa faɗar Allah ne maɗaukakin sarki.
Tun tana tunanin har bacci yayi awon gaba da ita. Kiran asuba na farko ne ya tayarda ita inda ta zame jikinta daga jikin Kabeer ta fice daga part (ɓangaren) nashi, saboda wannan na daga cikin al’adarta sai dai bansani ba don yara take hakan ko ra’ayinta ne.
Bayan tayi wanka ne tayi sallah ta zauna lazimi wanda ba ita ta tashi ba sai da gari ya yi haske misalin 7:15 kana ta shiga kitchen (madafi) domin haɗa kalaci. Zuwa 9:00 ta kammala komai har tayi wanka ta kimtsa Farha, Suleiman da Azeema sun fito fes dasu sai k’amshi suke zubawa.
A falonshi ta shimfiɗa babbar dadduma sannan ta jera duka kayan, Farha ta kallo tana mai bata umurnin taje ta kira Zainab suci abinci ita ko ta shiga uwar ɗaka domin fito da maigidan.
Yana jin motsinta ya yi lamo tamkar mai bacci, bakin gadon taje ta zauna sannan ta had’a hannunshi da nata tana murza ɗayan hannun, saurin janyota ya yi ta faɗo saman jikinshi sai sissinarta yake yi ta ko’ina.
“Haba Abban Farha karka ɓatan kwalliya don Allah, kuma ka tashi abinci ya kammalu kai muke jira”.
“Kwalliyarki ko tawa, saboda wa dama ake yin kwalliyar?”.
“Tabbb na yima kwalliya sanda nayi yanzu kam ina yine kawai saboda sabo da hakan”.
Murmushi ya yi kana ya mik’o hannu ta kama ya tashi zaunen yace’ “Hafsat rigima, gaki kullum sai kyawo kike k’arawa tamkar wata sabuwar amarya”.
“Uhmmm wai daga baya kenan anyi sadaka da karuwa, ni dai muje karka fara zantukan naka da ba tasiri zasuyi ba”.
Hannu ya mik’a zai cafkota ta yi saurin fita daga ɗakin tana murmushi inda shima ya fito falon fuskarshi a sake cikin walwala da nishaɗi.
Cikin wani irin ɗaure fuska ta gayar da shi tana cin magani tana kimbure_kumbure tamkar mai ciwon hak’ori, amsawa ya yi yana mai ɗan ɗauke kanshi zuwa ga yaran yana gaisawa dasu da ɗai ɗaya sannan ya ɗauki Azeema yana mata wasa har yakai zaune ya ɗorata saman cinyarshi.
Mamaki ne kwance fal a fuskarshi haɗe da y’ar damuwa, ya rasa sanin har sai yaushe ne zata fahimci cewa akwai CANJIN YANAYI, har kullum sai ya yi yunk’urin yin magana sai yaga abin tamkar cin fuska ne, yafi so ta fahimci yanayi ya canja da kanta.
Hakan suka ci abinci cikin kwanciyar hankali har suka yi hamdala. Suleiman ya kalla yace’ “ya kamata yau muɗan fita yawon shan iska ko?”.
Farha ce ta karɓe da cewa’ “Abba shan ice cream dai”.
Dariya suka yi dukansu banda Zainab data ɗauke kanta tamkar bataji me suke faɗa ba.
Tsam ta tashi ta shiga ɗaki ta ɗauko babban gyalenta ta fito da k’aramar jaka a hannunta. “Abba kai kace Umma ta bimu can ashkilim?”.
“Kai Azeema ba dai kishi ba, to ni gidan Anty Sis (Mama Sultan) zaku sauke ni ba can ashkilim ba, ai bakin naki ne ashkilim”.
Nan dukansu suka dinga mata dariya ita ko ta wangale baki sai kuka sai da Abban ya lallasheta sannan ta nutsu.
Nan ya cewa Zainab “to mu zamu fita, ko akwai wani abin na buk’ata da za’a siyo maki?”.
Kai kawai ta girgiza sannan ta tashi fuu tayi ɗakinta. Hakan suka haɗa suka fice daga gidan aka sauke Hafsat gidan Anty Sis su ko suka wuce gurin tasu siyayyar shi da yaranshi.
Da sallama ta shiga gidan inda Anty Sis ta saki baki sannan ta taryota tana mai yi mata kirarin’ “uwargida sarautar mata, an buga an barki uwa gun Farha madubin Abban Farha, farar mace alkyabbar mata haska gida komai duhunshi”.
Dundu Hafsat ta kaiwa Anty Sis tana murmushi, “bansan lokacin da kika tashi daga Anty Sis kika koma marok’iya ba, wannan kirarin ai sai amarya Zainab don mu yanzu mun tsufa”.
Harara ta sau mata kana ta rik’a hannunta suka k’arasa falon ta kawo mata ruwa da lemo sannan Anty Sis tayi gyaran murya, “kinsan wani abu Maman Farha?”.
“Sai kin faɗa Maman Sultan”.
“A duniya ina bak’in cikin naji mace tace wai ta tsufa don an mata Amarya, ballantana ke da banga abinda amaryar zata fiki dashi ba, kina sane da irin so, tattali, kulawa da kike samu gun Kabeer ko amarya bazata same shi ba, kuma…..”.
Saurin tarar numfashinta ta yi tace’ “wannan ada can baya ne da nake ni kaɗai, yanzu kam way’annan abubuwa an rabasu kashi biyu an bawa amarya ɗaya”.
Hannu ta ɗaga zata make mata baki taja baya tana dariya, kana Maman Sultan ta ɗora da cewa’ “ya kamata kiyiwa Kabeer adalci don ni dai iya sanina banga CANJIN YANAYI a zaman takewarku ba, duk da yawancin mata suna ik’irarin cewa da wuya Namiji yayi aure baki ga canji ba, in har zakiyi la’akari yau shekararku ɗai_ɗai har shekara goma sha shida da aure, zuwan Zainab shekara biyu amma baki da wani laifi da zaki kama Kabeer dashi”.
“Ita kanta Zainab gwargwado kuna samun zaman lafiya tsakanin zamanta kewarku saboda bata da irin rainin nan da jin kan wasu amare”.
“A ganinki ba, tabbas bazan ce maki tana da raini ba, kuma gwargwado tana bani girmana, amma babbar matsalata da ita duk ranar girkinta sai naga CANJIN YANAYI daga gurinta tana wani iyayi a dole miji ya dawo hannunta, kuma sai kiga ranar nawa girki tana wani cin magani da wani ɗaukar kai irin tana nuna jin zafin kasancewarmu a tare dashi, har yaran sai kiga tana wani basar dasu”.
“Wannan na banza ne, in ma sanin daɗin Miji ne ai kin fita keda kika raineshi a hannunki tazo gidan ta hau naki rainon, ni fa kinga inda za’a samu matsala in Abban Sultan ya yi aure Amarya tace zata nuna min wannan iyayin ko jibgarta zan iya yi”.
Dariya sosai Hafsat ta dingi yi har da rik’e ciki, “to kinga nama fiki hak’uri anan don ni ko harara bata taɓa shiga tsakanina da ita ba sai dai na basar kawai”.
“Kai ke dai bari kawai kishi halitta ce da Allah ya jefo Mata dashi a duniya, amma wallahi sam kishiya bata da daɗi sai ka jure, kinma san me?”.
Kai Hafsat ta girgiza alamar a’ah, “zan so watarana ki tambayi Abban Farha mu kaiwa Anty Jidda ziyara kiji lakcar kishi da zama da kishiya kanta”.
“Ai kinsan ma ba zai hanani zuwa ba, saboda kaf cikin K’awayena yafi yarda dake, kinsan yanda akayi kika samu wannan matsayin?”.
“Sai kin faɗa”.
“Tun lokacin auren Zainab da kishi ya dinga saka ni k’aramar hauka, wanda a wannan lokacin ba wanda yayi nasarar kwantar min da hankali sai ke, to tun wannan lokacin yake baki babban matsayi wai kin ciri tuta”.
Nan suka yi dariya dukansu wanda yayi dai_dai da hon ɗin Abban Farha, nan suka tashi suka fice tare har suka gaisa da Kabeer ya bada ɗayan leda cewa a bawa Sultan su ko suka wuce Anty Sis ta shige gidan.
Tun tana tunanin har bacci yayi awon gaba da ita. Kiran asuba na farko ne ya tayarda ita inda ta zame jikinta daga jikin Kabeer ta fice daga part (ɓangaren) nashi, saboda wannan na daga cikin al’adarta sai dai bansani ba don yara take hakan ko ra’ayinta ne.
Bayan tayi wanka ne tayi sallah ta zauna lazimi wanda ba ita ta tashi ba sai da gari ya yi haske misalin 7:15 kana ta shiga kitchen (madafi) domin haɗa kalaci. Zuwa 9:00 ta kammala komai har tayi wanka ta kimtsa Farha, Suleiman da Azeema sun fito fes dasu sai k’amshi suke zubawa.
A falonshi ta shimfiɗa babbar dadduma sannan ta jera duka kayan, Farha ta kallo tana mai bata umurnin taje ta kira Zainab suci abinci ita ko ta shiga uwar ɗaka domin fito da maigidan.
Yana jin motsinta ya yi lamo tamkar mai bacci, bakin gadon taje ta zauna sannan ta had’a hannunshi da nata tana murza ɗayan hannun, saurin janyota ya yi ta faɗo saman jikinshi sai sissinarta yake yi ta ko’ina.
“Haba Abban Farha karka ɓatan kwalliya don Allah, kuma ka tashi abinci ya kammalu kai muke jira”.
“Kwalliyarki ko tawa, saboda wa dama ake yin kwalliyar?”.
“Tabbb na yima kwalliya sanda nayi yanzu kam ina yine kawai saboda sabo da hakan”.
Murmushi ya yi kana ya mik’o hannu ta kama ya tashi zaunen yace’ “Hafsat rigima, gaki kullum sai kyawo kike k’arawa tamkar wata sabuwar amarya”.
“Uhmmm wai daga baya kenan anyi sadaka da karuwa, ni dai muje karka fara zantukan naka da ba tasiri zasuyi ba”.
Hannu ya mik’a zai cafkota ta yi saurin fita daga ɗakin tana murmushi inda shima ya fito falon fuskarshi a sake cikin walwala da nishaɗi.
Cikin wani irin ɗaure fuska ta gayar da shi tana cin magani tana kimbure_kumbure tamkar mai ciwon hak’ori, amsawa ya yi yana mai ɗan ɗauke kanshi zuwa ga yaran yana gaisawa dasu da ɗai ɗaya sannan ya ɗauki Azeema yana mata wasa har yakai zaune ya ɗorata saman cinyarshi.
Mamaki ne kwance fal a fuskarshi haɗe da y’ar damuwa, ya rasa sanin har sai yaushe ne zata fahimci cewa akwai CANJIN YANAYI, har kullum sai ya yi yunk’urin yin magana sai yaga abin tamkar cin fuska ne, yafi so ta fahimci yanayi ya canja da kanta.
Hakan suka ci abinci cikin kwanciyar hankali har suka yi hamdala. Suleiman ya kalla yace’ “ya kamata yau muɗan fita yawon shan iska ko?”.
Farha ce ta karɓe da cewa’ “Abba shan ice cream dai”.
Dariya suka yi dukansu banda Zainab data ɗauke kanta tamkar bataji me suke faɗa ba.
Tsam ta tashi ta shiga ɗaki ta ɗauko babban gyalenta ta fito da k’aramar jaka a hannunta. “Abba kai kace Umma ta bimu can ashkilim?”.
“Kai Azeema ba dai kishi ba, to ni gidan Anty Sis (Mama Sultan) zaku sauke ni ba can ashkilim ba, ai bakin naki ne ashkilim”.
Nan dukansu suka dinga mata dariya ita ko ta wangale baki sai kuka sai da Abban ya lallasheta sannan ta nutsu.
Nan ya cewa Zainab “to mu zamu fita, ko akwai wani abin na buk’ata da za’a siyo maki?”.
Kai kawai ta girgiza sannan ta tashi fuu tayi ɗakinta. Hakan suka haɗa suka fice daga gidan aka sauke Hafsat gidan Anty Sis su ko suka wuce gurin tasu siyayyar shi da yaranshi.
Da sallama ta shiga gidan inda Anty Sis ta saki baki sannan ta taryota tana mai yi mata kirarin’ “uwargida sarautar mata, an buga an barki uwa gun Farha madubin Abban Farha, farar mace alkyabbar mata haska gida komai duhunshi”.
Dundu Hafsat ta kaiwa Anty Sis tana murmushi, “bansan lokacin da kika tashi daga Anty Sis kika koma marok’iya ba, wannan kirarin ai sai amarya Zainab don mu yanzu mun tsufa”.
Harara ta sau mata kana ta rik’a hannunta suka k’arasa falon ta kawo mata ruwa da lemo sannan Anty Sis tayi gyaran murya, “kinsan wani abu Maman Farha?”.
“Sai kin faɗa Maman Sultan”.
“A duniya ina bak’in cikin naji mace tace wai ta tsufa don an mata Amarya, ballantana ke da banga abinda amaryar zata fiki dashi ba, kina sane da irin so, tattali, kulawa da kike samu gun Kabeer ko amarya bazata same shi ba, kuma…..”.
Saurin tarar numfashinta ta yi tace’ “wannan ada can baya ne da nake ni kaɗai, yanzu kam way’annan abubuwa an rabasu kashi biyu an bawa amarya ɗaya”.
Hannu ta ɗaga zata make mata baki taja baya tana dariya, kana Maman Sultan ta ɗora da cewa’ “ya kamata kiyiwa Kabeer adalci don ni dai iya sanina banga CANJIN YANAYI a zaman takewarku ba, duk da yawancin mata suna ik’irarin cewa da wuya Namiji yayi aure baki ga canji ba, in har zakiyi la’akari yau shekararku ɗai_ɗai har shekara goma sha shida da aure, zuwan Zainab shekara biyu amma baki da wani laifi da zaki kama Kabeer dashi”.
“Ita kanta Zainab gwargwado kuna samun zaman lafiya tsakanin zamanta kewarku saboda bata da irin rainin nan da jin kan wasu amare”.
“A ganinki ba, tabbas bazan ce maki tana da raini ba, kuma gwargwado tana bani girmana, amma babbar matsalata da ita duk ranar girkinta sai naga CANJIN YANAYI daga gurinta tana wani iyayi a dole miji ya dawo hannunta, kuma sai kiga ranar nawa girki tana wani cin magani da wani ɗaukar kai irin tana nuna jin zafin kasancewarmu a tare dashi, har yaran sai kiga tana wani basar dasu”.
“Wannan na banza ne, in ma sanin daɗin Miji ne ai kin fita keda kika raineshi a hannunki tazo gidan ta hau naki rainon, ni fa kinga inda za’a samu matsala in Abban Sultan ya yi aure Amarya tace zata nuna min wannan iyayin ko jibgarta zan iya yi”.
Dariya sosai Hafsat ta dingi yi har da rik’e ciki, “to kinga nama fiki hak’uri anan don ni ko harara bata taɓa shiga tsakanina da ita ba sai dai na basar kawai”.
“Kai ke dai bari kawai kishi halitta ce da Allah ya jefo Mata dashi a duniya, amma wallahi sam kishiya bata da daɗi sai ka jure, kinma san me?”.
Kai Hafsat ta girgiza alamar a’ah, “zan so watarana ki tambayi Abban Farha mu kaiwa Anty Jidda ziyara kiji lakcar kishi da zama da kishiya kanta”.
“Ai kinsan ma ba zai hanani zuwa ba, saboda kaf cikin K’awayena yafi yarda dake, kinsan yanda akayi kika samu wannan matsayin?”.
“Sai kin faɗa”.
“Tun lokacin auren Zainab da kishi ya dinga saka ni k’aramar hauka, wanda a wannan lokacin ba wanda yayi nasarar kwantar min da hankali sai ke, to tun wannan lokacin yake baki babban matsayi wai kin ciri tuta”.
Nan suka yi dariya dukansu wanda yayi dai_dai da hon ɗin Abban Farha, nan suka tashi suka fice tare har suka gaisa da Kabeer ya bada ɗayan leda cewa a bawa Sultan su ko suka wuce Anty Sis ta shige gidan.
Muje zuwa.

0 Response to "CANJIN YANAYI 3"
Post a Comment